Connect with us

Rahoto

Ta yaya za a magance Yajin aikin malaman jami a?

Published

on

Rahoton da nake ɗauke da shi a wannan wata zanyi Magana kan yanayin yadda ɗalibai kan samu tsaiko a karatunsu sakamakon yajin aiki da ma’aikata kan shiga ko kuma ƙungiyar malaman jami’oi.
Wannan lamari na yajin aiki zamu iya cewa ya zama wajibi akan duk wani ɗalibi cewa bai isa ya fara makaranta ba har ya gama ba tare da an tafi yajin aiki ba, ko dai ta ɓangaren ma’aikata ko kuma ɓangaren ƙungiyar ƴan ƙwadago.
A wani bincike da nayi akan yanayin yadda ɗalibai kan fuskanci Tsaiko wajen kammala karatunsu a dai dai wa’a din da aka ɗibar musu zasu kammala, to muddin jami’ar ko kwalejin ta gwamnati ce to bai isa ya gama a shekarun da aka tsara zai gama ba.
Tafiya yajin aiki a ɗan shekarun da ɗalibi yake karatu yakan kasance sau uku ko huɗu ko ma fiye da haka ya danganta da yadda yanayin yadda ma’aikata suke da buƙata a hannun gwamnati.
Haka zalika a binciken da nayi wasu ɗaliban kan fuskanci matsalar yajin aiki a duk shekara kenan idan ɗalibi yana karatun digiri wanda ake sa ran zai iya gamawa a shekara huɗu to sakamakon yajin aiki zai iya gamawa a shekara biyar ko shida.
Binciken ya kuma yi nazari kan yadda iyaye kan tsara wa ƴaƴansu tsarin karatu tun daga tushe amma da zarar an je matakin jami’a sai abin ya rushe ɗai ɗai ku ne masu sa’a sune suke kammalawa a dai dai lokacinsu shima sai sunyi yajin aiki sai dai ya danganta da yanayin daɗewar da za’a yi.
Lissafin shine ana kai yaro makarantar firamare yana shekara 7 zai kammala a shekara 6 sannan ya shiga sakandare ya kammala a shekara 6, daga bisani ya tafi jami’a inda ake sa ran yayi shekara 4, a lissafin kenan ɗalibi yana kammala karatun digiri da mafi karancin shekaru 23, to amma a wannan lokacin akan samu ɗalibi da zai kammala a shekaru 35 in banda lokacin tafiya bautar ƙasa shine yake rage shekaru.
Bayan matsalar yajin aiki da ɗalibai ke fuskanta a bangaren kammala karatu akan lokaci akwai ƙin fitar da sakamako akan lokaci, wanda kan sa ɗalibi ya rasa sanin makomarshi musamman ɗaliban da suke jarabawar ƙarshe daga nan sai tafiya yi wa ƙasa hidima.
Da kuma rashin cin nasarar jarabawar shiga zan jami’a wato JAMB haka kuma wurin jarabawar tantance ɗalibai shima ana samun rashin sa’a sai kaga yaro ya daɗe yana neman gurbin karatu a jami’o daban daban wanda anan shekaru suke tafiya.
a yanzu haka ƙungiyar malaman jami’oi suna cikin halin yajin aiki wanda sun shafe kusan wata ɗaya suna gudanar da wannan yajin aiki, sai dai har yanzu gwamnati bata biya musu buƙatunsu ba balle su janye, yajin aikin da suke, wannan shi yake kara kawo cikas a karatun ɗalibai.

Idan ba’a manta ba a baya bayan nan ƙungiyar ƙwadago suka shirya tafiya yajin aikin sai baba ta gani, wanda suke kira da a mayar musu da albashin ma’aikata ya zama mafi karanci dubu talatin (30000) a maimakon dubu sha takwas (18,000).
Wanda ƙungiyar wasu gwamnatocin jihohi sun amince wasu kuwa suka ce baza su iya biya ba, wanda daga ƙarshe gwamnatin tarayya ta bawa kwamitin ƙayyade albashi daman duba yuwuwar wannan ƙari, inda kwamitin ya amince da biyan wannan kuɗi hakan ya kawo karshen wannan yajin aiki da aka yi niyar tafiya.
Wannan tsaiko da ɗalibai kan samu a ɓangaren karatunsu yana janyo kyamatar shuwagabanni a zuciyoyinsu, da kuma shiga wani yanayi na ƙunci da takura kasancewar a lokacin da ɗalibi yake zaune a gida ba tare zuwa makaranta ba, ko kuma yana wata sana’a to yakan fada cikin mugayen tunani.
Shin ya ɗalibi yake ji a lokacin da aka ce an tafi yajin aiki, tambayar da nayi wa wani ɗalibi kenan dake jami’ar Tarayya dake Dutse wanda muka sakaye sunanshi inda yace ai shi wannan yajin aiki kamar shi aka cuta ma kasancewar ya gama karatu har yayi jarabawar ƙarshe amma kuma ya samu matsala wannan dalili yasa yanzu sai yayi zaman shekara guda a gida kafin ya tafi hidimar ƙasa to ire iren mu muna da yawa a cewar ɗalibin.

Su kuwa ƙungiyoyin ma’aikatu daban daban da na ƙwadago sun bayyana cewa babu wani mataki da ma’aikata zasu ɗauka don gwamnati ta sauraresu akan bukatunsu bai wuce su shiga yajin aiki ba, kamar yadda shugaban ƙwadago reshen jihar kano kwamared Kabiru Ado minjibir ya bayyana ga manema labarai.

Click to comment

Leave a Reply

Rahoto

Akwai Yiwuwar Kasuwanci Ya Tsaya Cak A Najeriya

Published

on

Yayin da ya rage saura kwanaki goma kacal a dakatar da karɓar kuɗaɗe da aka sauyawa fasali a Najeriya, kasuwanci na fuskantar barazana cikin waɗannan kwaanaki.

Gwamnatin tarayya ta sauya fasalin naira 200, 500 da kuma naira 1,000 tare da sanya wa’adin ƙarshen watan Janairun da mu ke ciki a matsayin ranar karshe da za a daina karɓar tsofaffin kuɗi.

A sakamakon hakan ya sanya wasu da dama daga cikin ƴan kasuwa musamman a Kano cibiyar Kasuwanci, su ka tsayar da ranar Laraba a matsayin ranar da za su rufe amsar tsofaffin kuɗin da aka sauya.

A ɓangaren ƙananan ƴan kasuwa kuwa sun sanya ranar Talata domin daina karɓar kuɗaɗen tare da ƙoƙarin shigar da waɗanda ke hannunsu zuwa gaba.

Wajen da gizo ke saƙar shi ne, har a yanzu babu wadatattun sabbin nairar a hannun mutane.

A wani bincike da Matashiya TV ta yi, ta gano wasu yankuna da ake sanya wani kaso kafin shigar da kuɗi ga masu sana ar POS.

Wata majiya taa tabbatar da cewar,ana karɓar naira 3,000 a matsayin caji idan mutum ya na so a tura masa naira 100,000.

Ko za a iya samun wadataccen kuɗin zuwa watan Fabrairu?

Tambayar da wasu mutaane ƴan Najeriya ke yi bayan ƙorafin rashin wadatar sabbin kuɗi a hannunsu.

Sai dai bankin Najeriya CBN ya ce ya kafa wani tsari da zai dinga karɓar tsofaffin kuɗin a mataki na ƙananan hukumomi na Najeriya.

Ko sabon tsarin na CBN ya fara aiki?

Har yanzu mutane na kokawa a dangane da batun sauyin kuɗin yayin da bankune ke cike don shigar da waɗand ake hannunsu zuwa asusun ajiya.

Ta yaya kasuwanci zai tsayaa cak a Najeriya?

Duba ga rashin wadatar sabbin kuɗin a hannun jama’a tare da ƙoƙarin mayar da tsofaffin zuwa bankuna, hada-hadar kasuwar na iya samun naƙasu duba ga yanayin da aka saba yin kasuwanci.

Da yawan ƴan kasuwa na amfani da takardar kuɗi wajen saye ko sayarwa a kasuwannin Najeriya.

Haka kuma mutane da ke siyayya na har yanzu akwai ƙaraancin kuɗaɗe a hannunsu yayin da ya rage saura kwanaki goma a dakatar da karɓar kuɗin a hukumance.

Ko za a iya samun sasdauci?

Akwai yuwuwar hakan duba ga cewa gwamnati ba ta yi aalbashi ba kuma ana kyautaa zaton biyan albashin da za a yi za a yi amfani da saabbin kuɗi qajen biya.

 

Continue Reading

Rahoto

Dala Bilayan 12 ake asara a Najeriya Sakamakon Rikicin Makiyaya da Manoma

Published

on

An samu rahoton asarar akalla dala biliyan 12 a Nijeriya, sakamakon rikicin manoma da makiyaya da ya mamaye sassa daban daban na kasar.

Daraktan kungiyar sa kai ta Mercy Corps, Ndubisi Anyanwu,ne ya sanar da hakan a ranar Talata a zantawarsa da manema labarai jim kadan bayan ganawa da jami’an gwamnati a garin Makurdi.

“a cewarsa sun yi kiyasin asarar akalla $12b a kowacce shekara sakamakon rikicin makiyaya da manoma. “Wannan wani babban al’amari ne kuma da zai iya shafar kasar baki daya,”

Anyanwu ya kara da cewa akwai bukatar a mayar da hankali kan rikici tsakanin makiyaya da manoma, yana mai cewa wannan ne ma dalilin da yasa kungiyar ta shiga cikin lamarin.

Ya yi nuni da cewa kungiyar Mercy Corps, da aka samar da ita karkashin hukumar USAID, ta mayar da hankali kan gina zaman lafiya na watanni 60 a Benue da wasu jihohin jihar.

Tun farko, shugabannin kananan hukumomi a jawabansu daban daban sun lissafa rashin aikin yi, rashin ababen more rayuwa daga cikin dalilan haddasa rikicin makiyaya da manoma.

Continue Reading

Rahoto

An samu asarar rayuka 415 a Najeriya daga watan Yuli zuwa yanzu

Published

on

Wasu Alkaluman bincike na nuni da cewar akalla mutane 415 aka kashe a Najeriya a watan Yulin da ya gabata sakamakon hare hare da kuma tashin hankalin da ake cigaba da samu a cikin kasar.

Rfi hausa ta rawaito cewa Wata kungiya da ta kira kan ta ‘Nigeria Mourn’ tace an fi samun kashe kashen dake da nasaba da hare haren Yan bindiga da rikicin yan tada kayar baya da kuma barayin shanu ne a Jihohin Kaduna da Borno da Katsina.

Alkaluman kungiyar sun ce daga cikin Jihohi 21 da aka kashe mutane 415, Jihar Kaduna ke sahun gaba da mutane 139, sai Barno mai 113, Katsina na da 80, Kogi 17, Nasarawa 13, Taraba 10, Benue 9 sai kuma Ebonyi mai 8.

Sauran sun hada da Zamfara mai mutane 7, Plateau 5, Edo da Akwa Ibom da Lagos na da bibiyu, sai kuma Jihohin Oyo da Imo da Rivers da Cross Rivers da Ogun da Bayelsa da Delta da kuma Kebbi dake da guda-guda.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: