Connect with us

Labaran ƙasa

Ana cigaba da zanga zanga kan cire Alƙalin Alƙalai a Najeriya

Published

on

Ƙungiyar Ɗaliban Najeriya reshen jihar Ogun sun gudanar da zanga zanga ta nuna ƙin amincewa da tuɓe alƙalin-alƙalai na ƙasar Najeriya.
Ɗaliban waɗanda suka nuna ƙin amincewarsu ta hanyar rubutu a allon riƙewa sun nuna damuwarsu kan yadda shugaban ƙasar ke iƙirarin yaƙi da cin hanci da rashawa.
a daidai lokacin ne kuma ƙungiyar lauyoyin Najeriya suka fara zanga-zanga kan matakin dakatar Babban Alkalin Najeriya Walter Onnoghen a gaban hedikwatar kungiyarsu (NBA) a Abuja ranar Litinin.

Masu zanga-zangar sun ce suna so ne Shugaba Muhammadu Buhari ya soke matakin dakatar da babban alkalin kasar.

A ranar Juma’a ne Shugaba Buhari ya dakatar da Mista Onnoghen bayan kotun da’ar ma’aikata (CCT) ta umarce shi da ya yi hakan saboda tuhumarsa da kin bayyana kadakorinsa.

Haka kuma shugaban ya rantsar da Mai Shari’a Ibrahim Tanko Mohammed a matsayin mukaddashin babban alkalin kasar.

Lauyoyin sun bukaci kungiyar NBA da ta fara yajin aiki kuma hukumar da ke kula da bangaren shari’ar da ta dakatar da sabon mukaddashin Alkalin Alkalin.

Yayin da suke zanga-zanga, an samu wani ayarin masu zanga-zanga da ya isa wurin, inda suke goyon bayan matakin Shugaba Buhari na dakatar da Onnoghen.

a wani cigaban kuma An girke ‘yan sanda a gaban hedikwatar kungiyar NBA da ke Abuja ranar Litinin
A safiyar ranar Litinin, an girke ‘yan sanda a gaban hedikwatar kungiyar NBA, inda mambobin suka yi wani taron don tattauna batun dakatar da Alkalin Alkalin.

Kungiyar lauyoyin ta kira wani taron gaggawa a ranar Litinin, bayan Shugaba Buhari ya dakatar da Mista Onnoghen.

Daya daga cikin lauyoyin da suka shiga zanga-zangar, sun ce Shugaba Buhari bai bi ka’ida ba wajen dakatar da alkalin.

Ya ce gwamnati ta nuna son kai don ya kamata ne kafin shugaban ya dauki matakin sai ya rubuta wa majalisar dattawan kasar.

Click to comment

Leave a Reply

Labaran ƙasa

Tafiya Yajin Aiki Ranar Laraba Babu Gudu Babu Ja Da Baya – NLC

Published

on

Kungiyar kwadago a Najeriya NLC ta ce ba gudu ba ja da baya wajen tafiya yajin aikin da ta tsara a ranar Laraba.

Kungiyar na ci gaba da mayar da hankali wajen hada kan ma’aikata don ganin an tafi yajin aikin nan da kwana biyu masu zuwa.

Matakin hakan ya biyo bayan tashi baram-baram da kungiyar ta yi bayan wani zama da wakilan gwamnatin tarayya a Abuja.

Matsin rayuwa bayan ƙara farashin litar mna fetur na daga dalilai da ya sa kungiyar za ta tafi yajin aikin.

A baya kungiyar ta shirya tafiya yajin aikin sai dai ta janye daga baya bayan sulhu da aka yi da bangaren gwamnatin tarayya.

Daga bisani kotu ta dakatar da kungiyar daga tafiya yajin aikin.

Ma’ajin kungiyar na ƙasa Hakeem Ambali ya shaida yadda gwamnatin ta yi watsi da zama zaman da aka tsara a ranar Juma’a.

A halin yanzu kungiyar na cigaba da samun goyon bayan ma’aikata don tafiya yajin aikin gama gari a ranar Laraba.

Karin albashi da raba tallafi na daga cikin muradun da kungiyar ta saka a zaman da aka yi da farko.

Continue Reading

Labaran ƙasa

NNPC Ta Sanar Da Sabon Farashin Man Fetir A Jihohin Najeriya

Published

on

Kamfanin man fetir na kasa Najeriya NNPC ya sanya sabon farashin da za a dinga sayar da man fetir a kasar, farashin shi ne daga Naira 488 zuwa 555 ma fi kololuwa.

Wannan yana zuwa ne awanni kadan bayan da sabon shugaban kasa Bola Tinubu ya sanar da janye tallafin na man fetir a fadin kasar.

A yau Laraba ne da safe jami’an hukumar ta NNPC suka ya zama, kuma a karshe suka yanke hukuncin cewa farashin man a manya, matsakaita da kananan wuraren sayarwa zai karu.

Kuma sanarwar ta umarcin dukkanin yan kasuwa da su gyara farashin sayar da man fetir din a dukkan jihohin fadin Najeriya.

Kafin yanzu akwai jita-jitar da aka yi ta cewa za a kayyade farashin man nan ba da dadewa ba, an kuma saki sabuwar takardar jadawalin farashin man na mabanbantan yankunan siyasar Najeriya daga hukumomin.

A cikin takardar kuma an umarci dukkan masu kasuwancin man, da rungumi sauyin nan take ba da bata lokaci ba daga yau Laraba 31 ga watan Mayun shekara ta 2023.

Continue Reading

Labaran ƙasa

Jami’an NSCDC Sun Kama Mutane 93 Da Ake Zargin Su Da Aikata Laifuka A Kano

Published

on

Hukumar ba da kariya ga fararen hula ta tabbatar da kame mutum 93 da ake zargi da aikata laifuka tsakanin watan Janairu zuwa Maris na wannan shekara.

Babban kwamandan hukumar na Jihar Kano malam Adamu Salihu shine ya tabbatar da hakan a lokacin zantawarsa da kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a yau juma’a
Adamu ya tabbatar da cewa daga cikin mutanan da hukumar ta kama ta gurfanar da 29 a gaban kotu yayin da ake cigaba da gudanar da bincike akan mutum 57 kafin gurfanar da su a gaban kuliya.

Babban kwamandan ya ba da tabbacin cewar hukumar na cigaba da gudanar da aiki kamar yadda doka ta tanada, na bada kariya ga al’umma.

Adamu Salihu ya kuma bukaci hadin kan al’umma da su zamto masu bawa jami’an tsaro hadin kai tare da bayanai domin a cewarsa al’amarin tsaro ya shafi kowa da kowa ne ba iya jami’an tsaro ba.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: