A wata ƙididdiga da Hukumar da ke kula da cututtuka masu saurin yaɗuwa a Najeriya NCDC ta bayyana cewa tun daga lokacin da aka samu ɓullar cutar Lasa da beraye ke yaɗawa a tsakanin alumma wanda yanzu haka cutar ta hallaka aƙalla mutane 57 a jihohi daban daban na Najeriya.
Hukumar NCDC ta kuma bayyana cewa akwai masu fama da cutar ta Lassa a jihohi 19 na ƙasar, ta kuma tabbatar da gano mutane 275 cikin mutane kimanin 800 da ake kyautata zaton suna ɗauke da cutar., wanda yanzu haka ake basu kulawa ta musamman a cibiyoyin da ke kula da cutar.
Hukumar ta kuma bayyana cewa jihar Edo da Ondo sune suka fi masu yawan ɗauke da wannan cuta, inda a yanzu haka akwai kimanin mutane 40 dake ɗauke da wannan cuta kamar yadda hukumar ta bayyana.
Haka kuma hukumar ta bayyana cewa akwai jami’an kiwon lafiya dake ɗauke da cutar lassa a dai ƙasar ta Najeriya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: