Siyasa
Lokaci yayi da yakamata na huta cewar Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari

Siyasa
Ba Iya Yawan Ƙuri’u Ne Ke Sanya Mutum Cin Zaɓe Ba – Alhassan Ado Doguwa


Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa, ya bayyana cewa cin zabe ba yawan kuri’un da aka kada ba ne kawai, harda bin ka’idoji.

Doguwa ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a gidan Talabijin na Channels TV yayin da yake mayar da martani kan cece-kucen da ake tafkawa dangane da zaben 2023 a jihar Kano.
Ya ce zabuka a tsarin dimokuradiyya irin na Najeriya a kodayaushe suna kan tsari da ka’idoji, kuma tsayawa zabe bisa wadannan ka’idoji ne ke sa a samu ‘yanci da gaskiya.

Ya ce, a gare shi idan aka tambaye shi abin da ke faruwa a Kano, abin da ya saba faruwa ne, Kano ta kasance jiha ce mai ci gaba, mai fafutuka ta fuskar siyasa da akida.

Sannan ya kara da cewa ya kamata mutane su san cewa bawai a zabi mutum shike nuna yaci zabe ba har sai ya cika dukkan sharudan da za su saka ya zama shugaba ga al’umma.

Siyasa
Jam’iyyar NNPP Ta Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja


Jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar Kano ta gabatar da zanga-zangarta zuwa Abuja saboda abin da ta kira da ana neman soke nasararta a zaben 2023.

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa shugabannin NNPP sun ce idan har aka karbe gwamnatin Kano daga hannunsu, za a iya haddasa rikici.
A wani jawabi da Ladipo Johnson ya fitar a ranar Laraba, ya yi gargadi cewa wannan rigima za ta iya shafar har sauran kasashe na Afrika.

Shugaban mai binciken kudi ya karanto jawabin da shugaban jam’iyyar NNPP na rikon kwarya, Abba Kawu Ali ya rubuta a ofishin ECOWAS.

NNPP ta kuma yi tattaki zuwa ofishin jakadancin Amurka da na Birtaniyya da babban ofishin kungiyar EU ta tarayyar Turai a garin Abuja.

Shugabannin na NNPP sun ce daga hukuncin kotun sauraron karar zabe da na daukaka kara, ta fito cewa ana so a zalunci mutanen Kano.
Jawabin Abba Kawu Ali ya ce mafi yawan al’umma sun zabi Abba Kabir Yusuf na NNPP a watan Maris, amma ana shirye-shirye domin a tsige shi. Sai dai jam’iyyar ta ce bazatayi watsi da takardun CTC da aka fitar ba.
Siyasa
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Kori Ƴan Majalisar Dokoki 11 Na Jam’iyyar PDP A Filato


Kotun daukaka kara da ke zamanta a birnin tarayya Abuja ta soke zaben ‘yan majalisar dokokin Jihar Filato 11 na jam’iyyar PDP, inda ta tabbatar da na jam’iyyar APC a matsayin wadanda suka samu nasarar.

A wani hukunci da kotun ta yanke karkashin jagorancin mai shari’a Oko Abang a ranar Juma’a, sun bayyana cewa kuri’un da dakatattun ‘yan majalisar suka samu ba su halarta ba a zaben ranar 18 ga watan Maris 2023.


Alkalin ya bayyana cewa jam’iyyar ta PDP ta sabawa dokar sashe na 177 na kundin mulkin Najeriya na shekarar 1999, kuma hakan ya sanya ba ta cancanci tsayar da ‘yan takarar ba.

A hukuncin kotun ta tabbatar da ‘yan takarar na jam’iyyar APC a matsayin wadanda suka samu nasarar a zaben.
Bayan yanke hukuncin a halin yanzu jam’iyyar APC ce ke da rinjaye a majalisar ta dokokin Jihar ta Filato.
-
Mu shaƙata10 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Labarai8 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?