Rahoto
Kun san ma’anar jagaliya a siyasa?


Jagaliya na nufin biyayya ko goya baya ga duk wani shugaba, ko wani ɗan takara mai neman wata kujera, ko kuma wani mai muƙami irin na siyasa akan duk wani ra’ayi mai kyau ko akasin sa dan samun biyan bukatar kai batare da la’akari da illa ko amfanin wannan lamari ga al’umma ba.
Ɗanjagaliya kuma na nufin duk mai yin siyasar banbaɗanci ga ɗan takara ko wanda ake bashi kayan maye da nufin sha ya bugu ya aikata abinda bai dace ba, dan biyan buƙatar wani ɗan takara ko mai riƙe da muƙamin siyasa.
Illar harkar jagaliyanci

Ɗan jagaliya a ko da yaushe yana yin abin da zai farantawa mai gidanshi rai ne, saboda biyan buƙatarshi da iyalan sa ba don cigaban al’umma ba, duk matsayin sa a gwamnati , komai zurfin ilimin sa komai matsayin sa a mataki na siyasa, koda kuwa ya tara miliyoyin kuɗaɗe.
Ina ɗan jagaliya ya sa gaba ?
Abin tambaya anan shine ɗan jagaliya da ake bashi kayan maye da yawo da makami ko ya sari abokin hamayya wato ɗan wata jam’iya me ribarsa a rayuwa, ?.
Mafi aka sari da zarar ɗan jagaliya ya aikata wani laifi aka kamashi, to iyayen gidansa ne suke karɓo shi daga hannun ƴan sanda, to amma fa shima sai uban gidan nashi ya sanshi shine zai tsaya masa.
Me makoman ɗan jagaliya a rayuwa ?
Ɗan jagaliya bashi da tsari na cigaba a rayuwa na yadda zai gina rayuwarshi kamar yadda yake ƙoƙari wajen ganin ya gina rayuwar uban gidanshi da iyalansa.
Dalili kuwa shi bai je makaranta ba, sannan bai koyi wata sana’ar dogaro da kai ba, ta wace hanya zai gina rayuwarshi face lalata rayuwarshi ta hanyar shaye shaye, da sare sare,.
A ko da yaushe ana kiraye kiraye kan matasa su kauce wa bangar siyasa, kamar yadda ƙungiyoyi na ciki da waje ke ta kiraye kiraye amma sam saƙon baya zuwa gare su, kasancewar basa bibiyan kafafen yaɗa labarai don jin saƙonnin da ake isar musu.
A wannan lokaci nima ina isar da wannan saƙo ne ga wanda suke assasa wannan harka ta jagaliyanci da matasa ke faɗawa.
Abin da ya janyo hankali na kan wannan batu shine ganin muna dab da yin zaɓen 2019, ta ƙasa baki ɗaya sai gashi a zagayen da ƴan takara kan yi ƙananan hukumomi , ko Mazaɓu don neman magoya baya, sai gashi an fito da wani sabon salo na ƙwace a loƙacin da ake gudanar da wannan gangami, wannan abu ya ta’azzara a wannan lokaci wannan ba ƙaramin barazana bane ga alumma da ma su kansu matasan.
Jami’an tsaro na iya ƙoƙari wajen daƙile wannan matsala amma abin kamar ba’ayi kasancewar kullum ya kan zo da sabon salo ne.
Wace gudunmawa kafafen Yaɗa labarai zasu bayar wajen wayar da kan matasa da su guji harkar jagaliyanci ?.
Kafafen yaɗa labarai sun daɗe suna wayar da kan matasa kan illar jagaliyanci, ta hanyar shirye shiryensu da suke gabatarwa musamman wanda suka shafi matasa.
Kamar yadda Mujallar matashiya take gabatar da wani shiri na musamman mai suna Don matasa a sashinta na talabijin dake youtube.
Sai dai inda gizo ke saƙar shi ne ba lallai bane a ce wanda ake shirin don su saƙon yana isa gare su.
Wace hanya za’abi wajen magance wannan matsala ta jagaliyanci ?.
Ni a ganina kamata yayi a sauke yaƙin neman zaɓe kawai na tara al’umma duk ɗan takara ya dinga yawon ziyara gida gida don neman a goya masa baya tare da bayyana manufofinsa, da kuma yin alƙawura na idan ya samu nasara ga aikin ta zai yi ko kuma ƙudiri da zai kai.
Ko kuma a koma bayyana manufofi ta hanyar kafafen yaɗa labarai da na sada zumunta.
Wannan shine ra’ayi na.


Rahoto
Akwai Yiwuwar Kasuwanci Ya Tsaya Cak A Najeriya


Yayin da ya rage saura kwanaki goma kacal a dakatar da karɓar kuɗaɗe da aka sauyawa fasali a Najeriya, kasuwanci na fuskantar barazana cikin waɗannan kwaanaki.

Gwamnatin tarayya ta sauya fasalin naira 200, 500 da kuma naira 1,000 tare da sanya wa’adin ƙarshen watan Janairun da mu ke ciki a matsayin ranar karshe da za a daina karɓar tsofaffin kuɗi.
A sakamakon hakan ya sanya wasu da dama daga cikin ƴan kasuwa musamman a Kano cibiyar Kasuwanci, su ka tsayar da ranar Laraba a matsayin ranar da za su rufe amsar tsofaffin kuɗin da aka sauya.

A ɓangaren ƙananan ƴan kasuwa kuwa sun sanya ranar Talata domin daina karɓar kuɗaɗen tare da ƙoƙarin shigar da waɗanda ke hannunsu zuwa gaba.

Wajen da gizo ke saƙar shi ne, har a yanzu babu wadatattun sabbin nairar a hannun mutane.

A wani bincike da Matashiya TV ta yi, ta gano wasu yankuna da ake sanya wani kaso kafin shigar da kuɗi ga masu sana ar POS.
Wata majiya taa tabbatar da cewar,ana karɓar naira 3,000 a matsayin caji idan mutum ya na so a tura masa naira 100,000.
Ko za a iya samun wadataccen kuɗin zuwa watan Fabrairu?
Tambayar da wasu mutaane ƴan Najeriya ke yi bayan ƙorafin rashin wadatar sabbin kuɗi a hannunsu.
Sai dai bankin Najeriya CBN ya ce ya kafa wani tsari da zai dinga karɓar tsofaffin kuɗin a mataki na ƙananan hukumomi na Najeriya.
Ko sabon tsarin na CBN ya fara aiki?
Har yanzu mutane na kokawa a dangane da batun sauyin kuɗin yayin da bankune ke cike don shigar da waɗand ake hannunsu zuwa asusun ajiya.
Ta yaya kasuwanci zai tsayaa cak a Najeriya?
Duba ga rashin wadatar sabbin kuɗin a hannun jama’a tare da ƙoƙarin mayar da tsofaffin zuwa bankuna, hada-hadar kasuwar na iya samun naƙasu duba ga yanayin da aka saba yin kasuwanci.
Da yawan ƴan kasuwa na amfani da takardar kuɗi wajen saye ko sayarwa a kasuwannin Najeriya.
Haka kuma mutane da ke siyayya na har yanzu akwai ƙaraancin kuɗaɗe a hannunsu yayin da ya rage saura kwanaki goma a dakatar da karɓar kuɗin a hukumance.
Ko za a iya samun sasdauci?
Akwai yuwuwar hakan duba ga cewa gwamnati ba ta yi aalbashi ba kuma ana kyautaa zaton biyan albashin da za a yi za a yi amfani da saabbin kuɗi qajen biya.
Rahoto
Dala Bilayan 12 ake asara a Najeriya Sakamakon Rikicin Makiyaya da Manoma


An samu rahoton asarar akalla dala biliyan 12 a Nijeriya, sakamakon rikicin manoma da makiyaya da ya mamaye sassa daban daban na kasar.

Daraktan kungiyar sa kai ta Mercy Corps, Ndubisi Anyanwu,ne ya sanar da hakan a ranar Talata a zantawarsa da manema labarai jim kadan bayan ganawa da jami’an gwamnati a garin Makurdi.
“a cewarsa sun yi kiyasin asarar akalla $12b a kowacce shekara sakamakon rikicin makiyaya da manoma. “Wannan wani babban al’amari ne kuma da zai iya shafar kasar baki daya,”

Anyanwu ya kara da cewa akwai bukatar a mayar da hankali kan rikici tsakanin makiyaya da manoma, yana mai cewa wannan ne ma dalilin da yasa kungiyar ta shiga cikin lamarin.

Ya yi nuni da cewa kungiyar Mercy Corps, da aka samar da ita karkashin hukumar USAID, ta mayar da hankali kan gina zaman lafiya na watanni 60 a Benue da wasu jihohin jihar.

Tun farko, shugabannin kananan hukumomi a jawabansu daban daban sun lissafa rashin aikin yi, rashin ababen more rayuwa daga cikin dalilan haddasa rikicin makiyaya da manoma.
Rahoto
An samu asarar rayuka 415 a Najeriya daga watan Yuli zuwa yanzu


Wasu Alkaluman bincike na nuni da cewar akalla mutane 415 aka kashe a Najeriya a watan Yulin da ya gabata sakamakon hare hare da kuma tashin hankalin da ake cigaba da samu a cikin kasar.

Rfi hausa ta rawaito cewa Wata kungiya da ta kira kan ta ‘Nigeria Mourn’ tace an fi samun kashe kashen dake da nasaba da hare haren Yan bindiga da rikicin yan tada kayar baya da kuma barayin shanu ne a Jihohin Kaduna da Borno da Katsina.
Alkaluman kungiyar sun ce daga cikin Jihohi 21 da aka kashe mutane 415, Jihar Kaduna ke sahun gaba da mutane 139, sai Barno mai 113, Katsina na da 80, Kogi 17, Nasarawa 13, Taraba 10, Benue 9 sai kuma Ebonyi mai 8.

Sauran sun hada da Zamfara mai mutane 7, Plateau 5, Edo da Akwa Ibom da Lagos na da bibiyu, sai kuma Jihohin Oyo da Imo da Rivers da Cross Rivers da Ogun da Bayelsa da Delta da kuma Kebbi dake da guda-guda.


-
Mu shaƙata8 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada4 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare4 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai4 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Labarai6 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?
-
Girke girke5 years ago
YADDA AKE LEMON SHINKAFA