Connect with us

Labaran ƙetare

Ƙungiyar kare Hakkin Bil Adama ta Human Rights Watch, ta zargi manyan ƙasashen duniya da kauda kansu kan yadda ake take hakkin Bil Adama

Published

on

 

sakamakon matsalolin     cikin gidan da suka addabe su.
Ƙungiyar ta sanar da haka ne yayin gabatar da        rahotan ta na wannan     shekara.
Rahotan ƙungiyar na bana yace ƙasar Amurka da    manyan ƙasashen Turai da suka mayar da hakkin Bil Adama a matsayin daya daga cikin manufofin su a ƙasashen waje tun lokacin yakin cacar baka, a yau sun kauda hankali daga kai.
Daraktan ƙungiyar Kenneth Roth, yace matakin            ƙalubalantar take hakkin Bil Adama na raguwa, inda yake komawa kan ƙungiyoyin cikin gida.
Roth yace shugaba Donald Trump na Amurka ya mayar da hankali wajen rungumar shugabannin dake kama karya,       rikicin ficewa daga kungiyar kasashen Turai ya mamaye Birtaniya, yayin da shugaban Faransa            Emmanuel Macron yana kalamai masu daɗi amma kuma baya iya aiwatar da su.
Daraktan yace ita ma       Angela Merkel wadda tayi fice wajen yaƙi da matsalar, yaƙi da masu tsatsauran ra’ayin cikin gida ya ɗauke mata hankali.
Rahotan ya yabawa ƙasashe 57 dake ƙungiyar ƙasashen Musulmi ta IOC da suka tashi tsaye domin        kalubalantar yadda ake cin zarafin yan kabilar    Rohingya a Myanmar, duk da yake kasashen basu ce komai ba kan yadda China ke cin zarafin Musulmi ‘yan kabilar Uighur., dake chana.

 

Click to comment

Leave a Reply

Labaran ƙetare

Ba Mu Da Niyyar Sauƙaƙa Haraji Akan Shigo Da Wasu Keɓaɓɓun Ma’adanai – Donald Trump

Published

on

Shugaban ƙasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa, babu wata niyya ko shiri na sauƙaƙa haraji akan ma’adanan Steel da kuma Aluminium sakamakon barazanar kasuwanci da ƙasar ke fuskanta daga takwarorinta.

Tun a watan Janairu ne dai shugaba Trump ya sanya haraji ga abokan kasuwanci da kuma masu shiga da kayayyaki, ciki har da ma’adanan Steel da kuma Aluminium.

Trump ya yi hakan ne dai da niyyar juya akalar ƙara samun kuɗi, da kuma tsoron kar shirye-shiryensa su jefa ƙasar cikin mashashsharar tattalin arziki.

Donald Trump ya shaidawa manema labarai cewa, bashi da niyyar cire tsarin harajin akan wasu keɓaɓɓun abubuwa.

Inda ma ya kuma ƙarfafa tunanin ruɓanya tsarin harajin nan da 2 ga watan Afrilu, dan magance matsalar kasuwanci da kuma sauran matsalolin a ɓangaren.

Trump ya ce zuwa yanzu ƙasar ta samu biliyoyin daloli da tsarin, kuma nan da watan Afrilun za su kuma samun kuɗaɗe masu yawan gaske.

Continue Reading

Labaran ƙetare

Harin Bom Ya Hallaka Mutane Fararen Hula 12 Tare Da Jikkata Wasu A Pakistan

Published

on

Wani mummunan harin bom daga ƴan ƙunar baƙin wake ya hallaka mutane fararen hula 12 a ƙasar Pakistan, cikinsu harda ƙananan yara shida.

Lamarin dai ya auku ne a Arewa maso Yammacin ƙasar a jiya Talata, yayin da wasu mahara su biyu su ka tuƙo mota ɗauke da abin fashewar zuwa wajen jami’an tsaro da ƴan sanda.

Gagarumin harin dai ya haifar da yaɗuwar hatsaniya tare da rikito da rufin wani Masallaci da ke kusa da wajen, a daidai lokacin da mazauna yankin su ke gudanar da buɗa bakin ibadar azumin watan Ramadan.

Harin kuma dai ya shafi cunkoson hada-hadar kasuwanci a wajen, tare da jikkata wasu mutanen da kuma lalata gine-gine.

Jami’an tsaro sun samu nasarar daƙile maharan daga shiga sansanin sojojin wajen, bayan sun yi artabun musayar wuta da su tare da hallaka mutane shida daga cikinsu.

Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai harin, sai dai a ƴan kwanakin nan ƙungiyar ƴan Taliban ta Pakistan ta tsaurara tsangwama ga jami’an tsaro, musamman a yankunan da su ka yi iyaka da ƙasar Afghanistan.

Continue Reading

Labaran ƙetare

Sabon Shugaban Ƙasar Ghana Mahama Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Tattalin Arziƙin Ƙasar

Published

on

Sabon shugaban ƙasar Ghana John Dramani Mahama ya sha alwashin gudanar da mulki na gaskiya da adalci a ƙasar.

Mahama ya bayyana haka jiya Talata a jawabin da ya yi jim kaɗan bayan rantsar da shi.

A cewarsa zai tabbatar da inganta bangaren tattalin arzikin ƙasar

Babban mai Shari’a a kasar ne ya rantsar da shu a Black Star Square da ke Accra babban birnin ƙasar

Dubban mutane ne su ja halarta domin shaida rantsuwar.

Mahama ya mulki kasar tsakanin shekarar 2013 zuwa 2017.

Mahama ya lashe zaben da kaso 56 a ranar 9 ga watan Disamban shekarar da ta gabata.

Shugaban Najeriya kuma shugaban kungiyar ECOWAS Bola Ahmed Tinubu na daga cikin manyan baki na musamman da su ka halarta.

Haka kuma akwai sauran manyan shugabannin kasashen Afrika da s ka hakarta.

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: