Labarai
Sakamakon zaɓen shugaban ƙasa – Jihar Anambra


Sunan Baturen zabe Fafesa Ungwachuku

Adadin ƙuri un da aka yi rijista 2.389.832
Ƙuri un da aka tantance 675.273

A 103

AA 57

AAC 124
ACPN 109
ADC 287
ADP 427
AGA 107
AGAP 349
ANN 45
ANP 26
ANIP 32
APA 596
APC 33.298
AUN 11
DMPP 47
CAP 6
GA 27
GPC 120
FRESH 54
FGP 45
GDPN 723
GPN 51
HDP 26
ID 28
JNPP 38
LP 52
LAJA 23
MMN 66
MPN 30
NAC 246
NCMP 17
NDCP 11
PDP 524.738
Labarai
Gwamnatin Najeriya Za Ta Shawo Kan Barazanar Tsaro Da Jami’o’in Ƙasar Ke Fuskanta


Ministan ilimi a Najeriya, Farfesa Tahir Mamman, ya jaddada yunkurinsa na tabbatar da ayyukan cigaba da za su daga likkafar bangaren ilimi a Najeriya.

Ya bayyana haka ne cikin wani jawabi da ya gabatar ga kwamitin mataimakan shugabannin jami’o’in Najeriya a Abuja yau Laraba.


Mamman ya tabbatarwa da wakilan cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu na da kyakkyawan yunkurin inganta harkokin koyo da koyarwa a daukacin jami’oin kasar nan.

Da yake nasa jawabin karamin ministan ilimi, Dr Yusuf Sununu, ya tabo batun matsalar rashin tsaro a jami’o’in Najeriya, wanda ya danganta batun da halin da ake ciki na garkuwa da aka yi da daliban jami’ar gwamnatin tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara.
Karamin ministan ya tabbatar da kyakkyawan yunkurinsu na kwararan matakai da aka dauka domin shawo kan al’amarin.
A cikin jawabinta, jagorar tawagar kuma shugabar kwamitin, Farfesa Lilian Salami ta nuna godiya da farin cikinta ga ministan bisa kasancewarsa mutum na farko a tarihi da aka nada minista lokacin da yake kan matsayin mataimakin shugaban jami’a.
Ms Salami ta hakaito wasu kalubale sa jami’o’in kasar ke fuskanta da su ka hadar da rashin isassun kudaden gudanarwa, wadatattun ma’aikata da sauransu.
Labarai
Ba Mu Tura Kowa Ba Ya Gana Da ‘Yan Bindiga A Zamfara – Badaru Abubakar


Gwamnatin Najeriya ta magantu dangane da zargin da gwamna Zamfara Dauda Lawal Dare ya yi na sulhu da ƴan bindiga a jiharsa.

Ministan tsaro a Najeriya Badaru Abubakar ne ya ce sam gwamnatin ba ta wani shirin yin sulhu da ƴan bindiga kamar yadda gwamnan ya yi zargi.
Gwamnatin ta musanta zargin ne a yau bayan da gwamnan Zamfara ya zargesu da yin sulhu kuma hakan na iya zama mayar da Hakan na zuwa ne bayan da aka yi garkuwa da wasu ɗalibai na jami’ar tarayya ta Gusau a jihar a makon jiya.

Gwamnatin ƙasar ta ce ba ta sanya wata ƙungiya ko hukuma tattaunawa da ƴan bindiga ba, a don haka zargin ba gaskiya ba ne.

Sannan gwamnatin ta himmatu wajen kuɓutar da ɗaliban da aka sace, kuma ana samun kyakkyawans akamako.

Mai magana da yawun ma’aikatar tsaro ta ƙsar Attari Hope ya ce shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarni domin ganin an samar da kyakkawan sakamako wajen ceto ɗaliban.
Labarai
Gwamnatin Najeriya Ta Sanya Gobe Laraba A Matsayin Ranar Hutu Ga ‘Yan Kasar


Gwamnatin Najeriya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu ga ma’aikata na ƙasar.

Haka na ƙunshe a wata sanawar da ma’aikatar harkokin cikin gida babban sakataren ma’aikatar ya fitar ranar Litinin a madadin ministan.
Sanarwar ta ce an bayar da hutun ne domin murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad Salallahu Alaihi Wasallam.

Gwamnatin ta buƙaci musullmi da su yi koyi da halayen Annabin tsira annabi Muhammad Salallahu Alaihi Wasallam musamman tausayi, jin ƙai, soyayya da haƙuri.

Sannan ta buƙaci ƴan ƙasar da su yi amfani da hutun wajen sanya ƙasar cikin addu’a musamman a kan harkokin tsaro da sauran al’amura.

Kuma gwamnatin ta buƙaci al’ummarta da su ci gaba da bai wa shugaba Bola Tinubu haɗin kai domin tabbatar da ayyukan ci gaba a ƙasar.
-
Mu shaƙata8 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada4 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare4 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai4 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Labarai6 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?
-
Girke girke5 years ago
YADDA AKE LEMON SHINKAFA