Labarai
Me ya sa aka sake zaɓar Buhari a karo na biyu?


Shugaba Muhammadu Buhari ya kasance mutumin da talakawa suke ƙauna har zuciyarsu, bisa yadda tsarin mulkinnsa na kare dukiyar al’umma.

A cikin mulkina na farko ya samar da ayyukan raya ƙasa kamar Tituna a wasu yankin, da samar da tsaro, duk da cewa wasu na ganin ya yi burus da wasu yankunan.
Cin hanci da rashawa shi ne abin da gwamnatin shugaba Buhari ke mayar da hankali wajen ganin an cafke duk wani da aka samu da badaƙalar.


Muhammadu Buhari shi ne shugaban da ya kafa tarihi, mutumin da ya fito da farin jinin talakawa, har ma ta kai mutane sun tura kuɗaɗensu don hidimta masa a lokacin takararsa ta farko.

A lokacin Mulkin shugaba Buhari Mujallar Matashiya ta kyallo wasu ayyuka da ya shimfiɗa ciki kuwa har da ƙoƙarin samawa matasa aikin yi ta hanyar N-POWER.

Inda kuma mabiyinda kuma abokin karawarsa na jam iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya ke binsa a yawan ƙuri u.
Muhammadu Buhari ya samu nasara a karo na biyu bayan da ya lashe zaɓen kujerar shugabancin ƙasar Najeriya a shekarar 2015
Muhammadu Buhari ya nemi takarar shugabancin ƙasar tun a ashekarar 2003 wanda bai samu nasara ba, hakan ya sa shi sake fitowa a shekarar 2007 haka zalika a lokacin abokin karawarsa Marigayi Umaru Musa Ƴar Adua ya samu nasara.
Hakan dai Muhammadu Buhari ya sake fitowa tarar shugabancin ƙasar a shekarar 2011 hakan dai a lokacin ma bai samu nasara ba sai a shekarar 2015 wandaya ci zaɓen tare da mataimakinsa Farfesa Ymi Osibajo.
Bayan zaɓen da aka gudanar a dukkan sassa na ƙasar Najeriya a ranar Asabar, Shugaba Muhammadu Buhari ya shi ne ɗan takara da yake da mafi rinjayen ƙuri u.
Haka kuma Muhammadu Buhari ya kasance mutumin da ya mutane suka aminta da gaskiyarsa da riƙon amana kamar yadda ya ke faɗa a yayin yaƙin neman zaɓensa.
Mujallar Matashiya ta bankaɗo wasu kalamai da shugabanke yi yayin da ya je yaƙin neman zaɓe a wurare da dama, Buhari na bayyana cewar gwamnatinsu za ta inganta harkokin noma da kiwo, samar da tsaro, buƙasa tattalin arziƙi da kuma walwalar jin daɗin ƴan ƙasa.
Za mu ci gaba idan halin ya yi.
Labarai
Zagon Kasan Da Kwankwaso Ya Yi Wa Jam’iyyar NNPP Ya Sa Ba Muyi Nasara A Kotuba- Alhaji Abbas


Babban jigo a jam’iyyar NNPP, Alhaji Abbas Onilewura ya zargi dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso kan rasa nasarar jam’iyyar a jihar Kano.

A jiya Laraba 20 ga watan Satumba kotun ta yanke hukunci inda ta tsige Gwamna Abba Kabir na jam’iyyar a matsayin gwamna.


Kotun kuma ta tabbatar da Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

Yayin da ya ke martani kan hukuncin, Abbas ya ce Kwankwaso ya siyar da jam’iyyar lokacin da ya ke tattaunawa da APC kan mukamin minista a Abuja.
Onilewura ya bayyana haka ne a yau Alhamis 21 ga watan Satumba a cikin wata sanarwa da ya fitar.
Ya ce zagon kasa da Kwankwaso ya yi wa jam’iyyar ce ya jawo rashin nasararta a hukuncin kotun da aka yanke a jiya.
Ya kara da cewa Wannan rashin nasara babbar asara ce a jam’iyyar mu kuma hakan ya faru ne saboda son rai na Kwankwaso wanda ya siyar da jam’iyyar.
Labarai
Gwamnatin Delta Ta Amince Da Rage Kaso 25 Na Kudin Jami’a A Jihar


Gwamnatin jihar Delta ta amince da rage kashi 25 na kudin makarantar daliban jami’a a jihar.

Wannan dai wani bangare ne na tallafin da gwamnatin za ta bai wa daliban kuma ya shafi jami’a hudu mallakin jihar.
Hakan na kunshe a wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan Festus Ahon ya sanyawa hannu ranar Laraba.

Sanarwar ta ce gwamnan ya bayar da umarnin bai wa ma’aikatan jihar tallafin naira dubu goma kowanne tsawon watanni uku.

Sannan an amince da kashe naira biliyan 5.522 ga ma’aikata 50,196 a matsayinalawus da aka yi musu karin matsayi.

Sannan gwamnatin za ta kashe naira biliyan goma wajen raba buhun shinkafa 17,000 da sama da buhu masara 60,000 ga marasa karfi.
Labarai
Cibiyar Kare Hakkin Yan Jaridu Ta Yi Allah-Wadai Da Cin Zarafin Yan Jarida A Kano


Cibiyar kare hakkin yan jarida ta duniya ta yi Alla wadai da cin zarafin yan jarida da wasu yan sanda su ka yi a Kano yau Laraba.

Salim Umar na jaridar Daily Trust da Zahradden Lawal na jaridar BBC an ci zarafinsu tare da lalata layan aikinsu yayin da us ke bakin aiki.
Babban jami’in kare hakkin yan jarida na duniya Melody Akunjiyan ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya aikewa manema labarai a yau.

Cibiyar ta ce abin takaici ne ganin yadda yan sandan su ka nuna rashin kwarewa ta hanyar cin zarafin yan jaridan yayin da su ke bakin aiki.

Cibiyar ta bukaci hukumar yan sanda ta kasa da su kula tare da kiyayewa a gaba wajen cin zarafin yan jarida musamman idan aiki ya hadasu da jami’an yan sanda.

Haka kuma cibiyar ta bukaci da aka ci gaba da bai wa yan sanda horo yadda za su dinga mu’amala da yan jarida tare da mutunta darajar dan adam.
-
Mu shaƙata8 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada4 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare4 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai4 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Labarai6 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?
-
Girke girke5 years ago
YADDA AKE LEMON SHINKAFA