Rahoton da mujallar matashiya take samu a yanzu haka, wata babbar kotun jihar Taraba ta dakatar da ɗan takarar jam’iyyar APC a zaɓen gwamna a jihar Taraba, kotun ta dakatar da ɗan takarar ne mai suna, Alhaji Sani Abubakar Ɗanladi daga tsayawa takarar bayan da aka yi zargin bayyana shekarun ƙarya a takardun da ya miƙawa hukumar zaɓe mai zaman kanta. Lamarin ya faru ne an saura kwanaki uku a gudanar da zaɓen gwamnoni da na ƴan majalisar jiha.
Idan ba’a manta ba wata kotu ta bada irin wannan makamancin umarnin ƙwace takarar mai neman gwamnan kano a inuwar jam’iyar PDP Engr Abba kabir yusif, amma shi ana zargin an tafka kura kure a zaɓen fiɗɗa gwani (primary Election).

Leave a Reply

%d bloggers like this: