Connect with us

Siyasa

Bana jin daɗin rabuwa da mutane na, kuma a shirye nake don ɗinke ɓarakar da ke tsakaninmu ko da kuwa Ganduje ne

Published

on

Tsananin tashin hankali na shiga yayin da na rabu da magoya bayana – Kwankwaso

Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma Sanatan Kano ta tsakiya Rabi u Kwankwaso ya bayyana cewar ba ya faɗa da kowa, kuma ko da ya ɓatawa wani zai iya dawowa don su shirya.

Sanata Kwankwaso dai ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi ta awanni biyu a kafafen yaɗa labarai na Kano, ya ce bai ji daɗin rabuwa da magoya bayansa ba, musamman waɗanda suke ganin bai kyauta musu ba.

“Duk wanda yake gani na ɓata masa zai iya dawowa don mu shirya” Inji Kwankwaso.

Cikin tattaunawa da ƴan jarida Kwankwaso ya bayyana cewar ba ƙaramin tashin hankali ya shiga ba sanadin rabuwa da magoya bayansa.

A cewar madugun kwankwasiyyar, dole ne sai an saɓa da mutane idan gangar siyasa ta kaɗa, amma hakan ba yana nufin an ɓata kwata kwata ba kenan.

A dai dai lokacin da ake dab da shiga zaɓen gwamnoni da ƴan majalisu, jihar kano dai siyasar ta ƙara tsami ganin yadda rikici ke tsakanin Sanata Rabi u Kwankwaso da kuma Gwamna Abdullahi Ganduje, sai dai kalaman nasu na nuni da cewar kowa ya saduda don dawowa a yi tafiya tare kamar yadda Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje ya bayyana.

Karanta a nan – https://matashiya.com/2019/03/08/a-shirye-nake-a-sulhuntamu-da-mai-gida-na-kwankwaso/

Click to comment

Leave a Reply

Siyasa

Kwamishina Yayi Barazana Ga Alkalai, Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Kano

Published

on

Kwamishinan kula da kasa a jihar Kano Adamu Aliyu Kibiya, ya yi barazana ga alkalan kotun sauraron kararrakin zaben gwamna.

Sannan kuma ya yi alkawarin tayar da rikici ga mazauna jihar, fiye da rikicin da al’ummar makotan jihar na jihohin Kaduna da Zamfara su ke fuskanta.

Mazaunan jihohin Kaduna da Zamfara dai su na fuskantar tashin hankalin hare-hare, kisa, da kuma garkuwa da su don karbar kudin fansa daga ‘yan bindiga.Wannan hare-haren dai yana faruwa sama da shekaru 10.

Aliyu ya yi zargin cewa, da akwai yiwuwar an bai wa alkalan cin hanci da rashawa dan su yi hukuncin da ba zai yi wa jam’iyyarsa dadi ba.

Kwamishinan ya yi barzanar cewa, idan alkalan kotun su ka yi hukuncin da bai bai’wa jam’iyyarsa ta NNPP nasara ba a korafin dake gabanta, to zasu biya bashin hakan da rayuwarsu.

Jam’iyyar APC da dan takarar gwamnanta Nasiru Yusuf Gawuna dai, su na kalubalantar nasarar da gwamnan jihar ta Kano Abba Kabir Yusuf ya samu a zaben da ya gabata.

Kotun sauraron kararrakin zaben dai har yanzu ba ta sanya ranar da za ta yanke hukunci a kan shari’ar ba, yayin da Aliyu Adamu ya yi wannan ikirarin lokacin da yake jawabi ga magoya bayan jam’iyyar NNPP yayin wata zanga-zanga da suka gudanar a ranar Alhamis.

Taron da aka gudanar kuma ya hadar da yin addu’a, don fatan yin nasara ga tsagin nasu a hukuncin da za a yanke.

Continue Reading

Siyasa

Jam’iyyar NNPP Ta Kori Kwankwaso

Published

on

Kwamitin zartaswa na kasa a jam’iyyar NNPP sun kori tsohon dan takarar shugabancin kasar jam’iyyar Sanata Rabiu Kwankwaso, biyo bayan kin bayyana da yayi a gaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar.

Idan za a iya tunawa shugabanvin jam’iyyar ya dakatar da Kwankwason, a taron jam’iyyar na kasa da ya wakana ranar 29 ga watan Ogustan da ya gabata a birnin Legas.

Babban kwamitin zartarwar jam’iyyar sun nada kwamitin ladabtarwa da zasu gayyaci tsohon gwamnan domin ya kare kansa, bisa tuhumar cin amanar jam’iyya da kuma wadaka da kudin yakin neman zaben jam’iyya cikin kwanaki biyar.

Kwamitin kuma yayi gargadin cewa gaza bayyana gaban kwamitin zai janyo korar Sanata Kwankwason daga jam’iyyar, bisa la’akari da tanadin da kundin tsarin mulkin jam’iyyar da aka yi wa kwaskwarima a shekarar 2022 ya yi.

Saboda haka, mai rikon kwaryar sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa Abdulsalam Abdulrasaq ya bayyana a cikin wani jawabi a yau Talata a birnin Legas cewa, kwamitin zartarwar jam’iyyar sun kori Kwankwason nan take, saboda kin girmama gayyatar kwamitin ladabtarwar.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito Abdulsalam Abdulrasaq yana sanar da hukuncin da suka dauka.

Continue Reading

Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Najeriya Ta Dakatar Da Kwankwaso Tsawon Watanni Shida

Published

on

Kwamitin amintattu a jam’iyyar NNPP a Najeriya sun sanar da dakatar da jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso daga cikinta.

Jam’iyyar ta naɗa Dakta Agbo Major a matsaayin shugaban jam’iyyar na riko da wasu mukamai 19.

An dakatar da Sanata Rabi’u Kwankwaso tsawon watanni shida daga jam’iyyar.

Kamfanin dillancin labarai naa ƙasa NAN ya ruwaito cewar dakatarwar ta biyo bayan wani taro da jam’iyyar ta gudanar a jihar Legas yau Talata.

Sakatare a kwamitin amintattu na jam’iyyar Babayo Muhammed Abdullahi ya bayyanawa manema labarai cewa sun dakatar da Kwankwaso bayan zargin cin dunduniyar jamiyyar wajen taimakawa shugaba Bola Tinubu.

Haka kuma sun dakatar da shi ne bisa dokar kundin tsarin gudanarwar jam’iyyar ya tanada.

Tun tuni jam’iyyar ta zargi Sanata Kwankwaso da cin dunduniyarta, wanda ta ce ya yi amfani da su ne wajen taimakawa siyasar Shugaba Bola Tinubu na Najeriya.Kwamitin amintattu a jam’iyyar NNPP a Najeriya sun sanar da dakatar da jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso daga cikinta.
Jam’iyyar ta naɗa Dakta Agbo Major a matsaayin shugaban jam’iyyar na riko da wasu mukamai 19.
An dakatar da Sanata Rabi’u Kwankwaso tsawon watanni shida daga jam’iyyar.
Kamfanin dillancin labarai naa ƙasa NAN ya ruwaito cewar dakatarwar ta biyo bayan wani taro da jam’iyyar ta gudanar a jihar Legas yau Talata.
Sakatare a kwamitin amintattu na jam’iyyar Babayo Muhammed Abdullahi ya bayyanawa manema labarai cewa sun dakatar da Kwankwaso bayan zargin cin dunduniyar jamiyyar wajen taimakawa shugaba Bola Tinubu.
Haka kuma sun dakatar da shi ne bisa dokar kundin tsarin gudanarwar jam’iyyar ya tanada.
Tun tuni jam’iyyar ta zargi Sanata Kwankwaso da cin dunduniyarta, wanda ta ce ya yi amfani da su ne wajen taimakawa siyasar Shugaba Bola Tinubu na Najeriya.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: