Labaran ƙetare
Ƴan makaranta na yin zanga-zanga
Gwamnatin Aljeriya ta ɗauki matakin rufe ilahirin jami’o’in ƙasar, makwanni biyu kafin fara hutunsu a hukumance, don daƙile aniyar dubban ɗaliban da ke shiga zanga-zangar adawa da tazarcen shugaba AbdelAziz Bouteflika, da yake yunƙurin yi.
Dubban jama’a dai na ci gaba da yin dandazo a birnin Algiers, tattare da aniyar tilasta kawo ƙarshen shugabancin Bouteflika na tsawon shekaru 20, da a yanzu ke neman wa’adi na biyu.
A wani Rahoton da mujallar matashiya ta samu na nuni da cewa jami’an tsaron ƙasar sun kame aƙalla masu zanga-zanga 195, da aikata laifukan fasa shaguna, da kuma tayar da hatsaniya.
A halin da ake ciki, sama da makwanni biyu ke nan shugaban na Aljeriya yana ƙasar Switzerland inda ake duba lafiyarsa.
Tun a shekarar 2013, Bouteflika ya daina fita cikin jama’a bayan kamuwa da ciwon mutuwar barin jiki.
Amma sai yau ya dawo ƙasar har kuma jami’an tsaro suka yi masa jerin gwanon taya shi murnar dawowa ƙasar sa.
Labaran ƙetare
Ya Kamata A Dinga Jefe Ƴan Luwaɗi Da Maɗigo – Shugaban Ƙasar Burundi
Shugaban kasar Burundi, Evariste Ndayishimiye ya bayyana matakin da ya kamata a rinka dauka kan masu neman maza waɗanda aka fi sani da ‘yan luwadi.
Evariste ya ce kamata ya yi a rinka jefe su da su da masu auren jinsi inda ya ce hakan ba wani laifi ba ne.
Shugaban ya bayyana haka ne yayin ganawa da ‘yan jaridu a ranar Juma’a 29 ga watan Disamba.
Ya ce kasarsa ba ta bukatar duk wani taimako daga kasashen Yamma a kokarin kakaba musu sharadin luwadi da madigo.
Har ila yau, shugaban ya ja aya a cikin littafin Inijla inda ya ce Ubagiji ya haramta neman jinsi kwata-kwata.
Ndayashimiye ya kara da cewa kasarsa bata bukatar fara tattauna magana kan ‘yan luwadi da masu auren jinsi.
Ya ce luwadi da madigo hanya ce a bayyane tsakanin hanyar gaskiya ta ubangiji da kuma hanyar bata ta shaidan.
Burundi na daga cikin kasashen Afirka da suka haramta luwadi wanda hakan ya sa aka sanya hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari.
Labaran ƙetare
Shugaban Ƙasar Madagaska Andry Rajoelina Ya Lashe Zaɓe A Karo Na Biyu
Shugaban ƙasar Madagaska Andry Rajoelina ya sake lashe zaɓe karo na biyu, duk da kuwa ƙauracewa yin zaɓen da ƴan tsagin masu hamayya suka yi a yankin kudu maso Gabashin ƙasar ta tsuburin Afirka.
Andry ya samu kaso 58.95 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa, wanda hukumar zaben ƙasar ta sanar a yau Asabar.
Ƴan takarkarun tsagin hamayya Siteny Randrianasoloniaiko da Marc Ravalomanana sun samu kashi 14.4 da kuma kashi 12. 1 kowannensu.
Ƴan takarkarun tsagin hamayya su goma sun yi kira ga magoya bayansu da su ƙauracewa yin zaɓen, duk da kuwa an sanya sunayensu a jikin takardar ƙuri’ar zaben da aka riga aka buga.
Hukumar zaɓen ta ce kaso 46 cikin 100 sun fito kaɗa ƙuri’a, amman ba a ga fuskar ko ɗaya daga cikin ƴan takarkarun hamayya 12 a wajen sanar da sakamakon zaɓen ba ranar da safiyar yau Asabar.
Ƴan siyasar tsagin hamayyar sun zargi shugaba Rajoelina da ƙoƙarin cigaba da mulki ta hanyar da bata dace ba, sun zargi shugaban da bai’wa kotuna da jami’an hukumar zaben cin hanci.
Labaran ƙetare
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Awanni Huɗu Kullum A Arewacin Gaza
Ƙasar Isra’ila ta amince a tsagaita wuta na awanni huɗu a kullum a arewacin Gaza, don a bai’wa fararen hula damar ficewa daga yankin.
Fadar gwamnatin Amurka ce ta sanar da hakan a yau Alhamis, duk da cewa shugaban ƙasar Joe Biden ya ce babu cikakkiyar tsagaita wuta.
Biden ya yabawa Fara-ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu bisa ɗan dogon hutu a faɗan, bayan tsawon wata daya da aka ɗauka ana fafata rikicin.
Sojojin Hamas da Isra’ila yanzu kowanne yana maɓoyarsa, kusa da inda ake gwabza faɗan a birnin Gaza, a yankin arewacin Zirin Gaza.
Mai magana da yawun sashin tsaron ƙasar John Kirby ya sanar da manema labarai cewa, Isra’ila za ta fara Ƙaddamar da Dakatar da faɗan na awanni huɗu a kullum a yankin na Arewacin na Gaza.
“Isra’ilawa sun sanar da mu cewa, ba za a samu aikin sojin su a yankin ba na tsawon lokutan da aka ɗauka, kuma hakan zai fara daga yau.”
-
Mu shaƙata1 year ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Labarai2 months ago
Mafi Karancin Sadaki A Najeriya Ya Koma Dubu 99,241
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini4 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida