Siyasa
PDP ta yi watsi da zaɓen cike gurbi da ake gudanarwa a Kano yau


Jam’iyyar PDP a jihar Kano ta bukaci Hukumar Zabe INEC da ta soke karashen zaben gwamnan Kano da ke gudana a yau asabar a wasu sassa na jihar Kano.

Shugaban riko na jam’iyyar a nan Kano Rabi’u Sulaiman Bichi ne ya bukaci hakan yayin wani taron manema labarai da ya kirawo a nan Kano.
Rabi’u Sulaiman yace abun da ake gudanarwa a Kano ba zabe bane, inda ya zargi cewa ana gudanar da zaben ba ta hanyar da ta dace ba.

Shugaban jam’iyyar ta PDP yace suna nan suna duba irin matakin da ya dace su dauka kafin ace an bayyana Wanda ya lashe zaben gwamnan Kano.

kamar yadda rahotonanni kee nunawa a wasu wuraren an samu ɓullar baƙin ƴan sara suka da ke tayar da hankula a wasu mazaɓun.

Siyasa
Son Kai Shi Zai Hana Kwankwaso Ya Zama Shugaban Kasa – Ganduje


Shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje, ya yi bayanin dalilin da yasa yake ganin tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP Rabi’u Musa Kwankwaso ba zai taba zama Shugaban kasa ba.

Da yake jawabi jiya Laraba a birnin tarayya Abuja, lokacin da tsohon dan takarar gwamnan jihar Bauchi karkashin jam’iyyar NNPP a zaben da ya gabata Sanata Halliru Jika ya bayyana komawarsa jam’iyyar APC, ya bayyana cewa tsantsar son kai shi zai hana Kwankwaso darewa kujerar shugabancin kasa.
Tsohon gwamnan na Kano har karo biyu ya kara da cewa, yanayin hakan ya bayu ne sakamakon gazawar Kwankwason, na kasa tsayar da bigiren akidar siyasar jam’iyya tsawon shekaru.

Ganduje ya bayyana Halliru Jika a matsayin jajirtaccen dan siyasa, ya kuma yi farin ciki da dawowarsa jam’iyyar APC, inda yace a baro jam’iyya da take mai kyau kuma mai kima a da can baya, kafin ‘yan kungiyar Kwankwasiyyah su zo su kwace ta kuma su gurbata ta.

A wani bangaren ya koka da koma bayan da jam’iyyar APC ta samu a jihar Bauchi, tare da alkawarin farfadowa da gina jam’iyyar. Da nufin sake shirin tunkarar kakar zabe ta 2027.

Halliru Jika wanda ya bar jam’iyyar ta NNPP zuwa APC tare da wasu ‘yan majalissun dokokin jihar da na tarayya, ya ce ya yanke shawar yin hakan ne bisa bukatar magoya bayansa a jihar ta Bauchi.
Siyasa
Kwamishina Yayi Barazana Ga Alkalai, Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Kano


Kwamishinan kula da kasa a jihar Kano Adamu Aliyu Kibiya, ya yi barazana ga alkalan kotun sauraron kararrakin zaben gwamna.

Sannan kuma ya yi alkawarin tayar da rikici ga mazauna jihar, fiye da rikicin da al’ummar makotan jihar na jihohin Kaduna da Zamfara su ke fuskanta.
Mazaunan jihohin Kaduna da Zamfara dai su na fuskantar tashin hankalin hare-hare, kisa, da kuma garkuwa da su don karbar kudin fansa daga ‘yan bindiga.Wannan hare-haren dai yana faruwa sama da shekaru 10.

Aliyu ya yi zargin cewa, da akwai yiwuwar an bai wa alkalan cin hanci da rashawa dan su yi hukuncin da ba zai yi wa jam’iyyarsa dadi ba.

Kwamishinan ya yi barzanar cewa, idan alkalan kotun su ka yi hukuncin da bai bai’wa jam’iyyarsa ta NNPP nasara ba a korafin dake gabanta, to zasu biya bashin hakan da rayuwarsu.

Jam’iyyar APC da dan takarar gwamnanta Nasiru Yusuf Gawuna dai, su na kalubalantar nasarar da gwamnan jihar ta Kano Abba Kabir Yusuf ya samu a zaben da ya gabata.
Kotun sauraron kararrakin zaben dai har yanzu ba ta sanya ranar da za ta yanke hukunci a kan shari’ar ba, yayin da Aliyu Adamu ya yi wannan ikirarin lokacin da yake jawabi ga magoya bayan jam’iyyar NNPP yayin wata zanga-zanga da suka gudanar a ranar Alhamis.
Taron da aka gudanar kuma ya hadar da yin addu’a, don fatan yin nasara ga tsagin nasu a hukuncin da za a yanke.
Siyasa
Jam’iyyar NNPP Ta Kori Kwankwaso


Kwamitin zartaswa na kasa a jam’iyyar NNPP sun kori tsohon dan takarar shugabancin kasar jam’iyyar Sanata Rabiu Kwankwaso, biyo bayan kin bayyana da yayi a gaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar.

Idan za a iya tunawa shugabanvin jam’iyyar ya dakatar da Kwankwason, a taron jam’iyyar na kasa da ya wakana ranar 29 ga watan Ogustan da ya gabata a birnin Legas.
Babban kwamitin zartarwar jam’iyyar sun nada kwamitin ladabtarwa da zasu gayyaci tsohon gwamnan domin ya kare kansa, bisa tuhumar cin amanar jam’iyya da kuma wadaka da kudin yakin neman zaben jam’iyya cikin kwanaki biyar.

Kwamitin kuma yayi gargadin cewa gaza bayyana gaban kwamitin zai janyo korar Sanata Kwankwason daga jam’iyyar, bisa la’akari da tanadin da kundin tsarin mulkin jam’iyyar da aka yi wa kwaskwarima a shekarar 2022 ya yi.

Saboda haka, mai rikon kwaryar sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa Abdulsalam Abdulrasaq ya bayyana a cikin wani jawabi a yau Talata a birnin Legas cewa, kwamitin zartarwar jam’iyyar sun kori Kwankwason nan take, saboda kin girmama gayyatar kwamitin ladabtarwar.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito Abdulsalam Abdulrasaq yana sanar da hukuncin da suka dauka.
-
Mu shaƙata8 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada4 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare4 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai4 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Labarai6 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?
-
Girke girke5 years ago
YADDA AKE LEMON SHINKAFA