Labarai
Za mu yi tafiya da Matasa a zangon na biyun mulkinmu – Ganduje



Daga Abba Anwar
Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewar sabuwar gwamnatinsa da za ta fara daga 29 ga Watan Mayu, 2019, za ta yi tafiya da matasa wajen gudanar da gwamnati. Bisa la’akari da irin gudummawar da matasan suke bayarwa wajen cigaban kasa.

Ya ce ya tabbatar matasan wannan jiha ba abinda yake gabansu illa ganin an samu cigaba mai dorewa a wannan jiha. Ya ce saboda haka “Ina yi musu albishir da cewa wannan sabuwar gwamnati mai shigowa za ta tafi da su ka’in da na’in.”

Gwamnan ya yi wannan albishir ne lokacin da shugabannin Majalisar Matasa Ta Kasa, wato “National Youth Council of Nigeria” karkashin jagorancin shugabansu na kasa, Bello Bala Shagari, ta kai masa ziyarar taya murnar sake samun nasarar zama gwamna a karo na biyu, a gidan gwamnatin jihar kano.

Ya ce saboda amincewa da yadda matasa ke kokari wajen ganin an samar da al’umma ta gari, hakan ta sa gwamnatinsa ke kokarin ganin an tallafi tafiya da kuma rayuwar matasan.
“Ina mai tabbatar muku da cewa mun ga irin kokarin da matasanmu na wannan jiha su ka yi lokacin zaben shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma zaben gwamna da zabubbukan ‘yan Majalisar Tarayya da na jiha,” in ji shi.
Ya ci gaba da cewa “Kasancewar irin wannan jajircewa da matasanmu su ka yi, ya nuna a fili cewar sun yunkuro sun nunawa duniya cewar lallai za a iya gogayya da su wajen gudanar da shugabanci na gari wanda zai amfani dukkan al’umma. Za mu yi wannan tafiyar da su saboda mu na da tabbacin cewa sun yunkuro saboda su bayar da ta su gudummawar wajen raya kasa da al’umma.”
Gandujen ya kara da cewa, saboda irin namijin kokarin da matasan su la nuna wajen kara samun tabbatuwar zaman lafiya, bayan kammala zabubbukan da a ka kammala kwanan nan, ya zama karin karfafa gwuiwa idan a ka nuna matasan su na da muhimmanci wajen gina kasa.
Wannan maganar ta gwamna Ganduje, kamar yadda shugaban Majalisar Matasan Na Kasa, Bello Bala Shagari ya bayyana, tabbatuwar gagarumar nasara ne da gwamnatin jihar Kano ke son assasa shi a wannan bangare na wannan kasa. Wanda kuma zai iya bazuwa zuwa ga dukkan sasaa na wannan kasa.
Shugaban ya kara da godewa gwamna Ganduje saboda hobbasa da gwamnan ya yi ta yi har sai da a ka samu tabbatuwar samar da shugabancin wannan Majalisar Matasan na farko daga yankin Arewa Maso Yamma na wannan kasa.
Ya kara yabawa Ganduje ganin yadda gwamnan ya rungumi harkokin Majalisar da matukar muhimmanci. “Haka nan kuma Alhamdulillah mun ga yadda Maigirma gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya samar da mukamai ga matasa a wannan zubin farkon na mulkinsa,” in ji shi.
Ya kara wata godiyar sabuwa jin cewa ga maganar da gwamnan ya yi wajen kara samar da gurabe ga matasa a juyowa ta biyu ta mulkinsa.
Ya ce “Maigirma gwamna tun ma kafin mu zo wannan waje, mun tabbatarwa da kan mu cewar za mu zo wajen gwamnan da ya dauki matasa da muhimmancin gaske. Alhamdulillah sai ga shi kuwa ka fitar da mu kunya ka tabbatarwa da kowannenmu cewar haka kake.”
Shagarin ya kara yabawa da ayyukan cigaban kasa da gwamnan Kanon yake jajircewa a kai, da yawun Majalisar Matasa ta Kasa din. Ya ce “Wannan Majalisa ta mu ta na mai tabbatar maka da goyon bayanmu kowane lokaci domin samun dorewar wannan mulki cikin nasara da kwanciyar hankali.”
Anwar shine Babban Sakataren Yada Labarai Na Gwamnan Jihar Kano
Labarai
Zagon Kasan Da Kwankwaso Ya Yi Wa Jam’iyyar NNPP Ya Sa Ba Muyi Nasara A Kotuba- Alhaji Abbas


Babban jigo a jam’iyyar NNPP, Alhaji Abbas Onilewura ya zargi dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso kan rasa nasarar jam’iyyar a jihar Kano.

A jiya Laraba 20 ga watan Satumba kotun ta yanke hukunci inda ta tsige Gwamna Abba Kabir na jam’iyyar a matsayin gwamna.


Kotun kuma ta tabbatar da Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

Yayin da ya ke martani kan hukuncin, Abbas ya ce Kwankwaso ya siyar da jam’iyyar lokacin da ya ke tattaunawa da APC kan mukamin minista a Abuja.
Onilewura ya bayyana haka ne a yau Alhamis 21 ga watan Satumba a cikin wata sanarwa da ya fitar.
Ya ce zagon kasa da Kwankwaso ya yi wa jam’iyyar ce ya jawo rashin nasararta a hukuncin kotun da aka yanke a jiya.
Ya kara da cewa Wannan rashin nasara babbar asara ce a jam’iyyar mu kuma hakan ya faru ne saboda son rai na Kwankwaso wanda ya siyar da jam’iyyar.
Labarai
Gwamnatin Delta Ta Amince Da Rage Kaso 25 Na Kudin Jami’a A Jihar


Gwamnatin jihar Delta ta amince da rage kashi 25 na kudin makarantar daliban jami’a a jihar.

Wannan dai wani bangare ne na tallafin da gwamnatin za ta bai wa daliban kuma ya shafi jami’a hudu mallakin jihar.
Hakan na kunshe a wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan Festus Ahon ya sanyawa hannu ranar Laraba.

Sanarwar ta ce gwamnan ya bayar da umarnin bai wa ma’aikatan jihar tallafin naira dubu goma kowanne tsawon watanni uku.

Sannan an amince da kashe naira biliyan 5.522 ga ma’aikata 50,196 a matsayinalawus da aka yi musu karin matsayi.

Sannan gwamnatin za ta kashe naira biliyan goma wajen raba buhun shinkafa 17,000 da sama da buhu masara 60,000 ga marasa karfi.
Labarai
Cibiyar Kare Hakkin Yan Jaridu Ta Yi Allah-Wadai Da Cin Zarafin Yan Jarida A Kano


Cibiyar kare hakkin yan jarida ta duniya ta yi Alla wadai da cin zarafin yan jarida da wasu yan sanda su ka yi a Kano yau Laraba.

Salim Umar na jaridar Daily Trust da Zahradden Lawal na jaridar BBC an ci zarafinsu tare da lalata layan aikinsu yayin da us ke bakin aiki.
Babban jami’in kare hakkin yan jarida na duniya Melody Akunjiyan ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya aikewa manema labarai a yau.

Cibiyar ta ce abin takaici ne ganin yadda yan sandan su ka nuna rashin kwarewa ta hanyar cin zarafin yan jaridan yayin da su ke bakin aiki.

Cibiyar ta bukaci hukumar yan sanda ta kasa da su kula tare da kiyayewa a gaba wajen cin zarafin yan jarida musamman idan aiki ya hadasu da jami’an yan sanda.

Haka kuma cibiyar ta bukaci da aka ci gaba da bai wa yan sanda horo yadda za su dinga mu’amala da yan jarida tare da mutunta darajar dan adam.
-
Mu shaƙata8 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada4 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare4 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai4 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Labarai6 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?
-
Girke girke5 years ago
YADDA AKE LEMON SHINKAFA