Labarin wasanni
Tabbas Zidane ƙwararren mai horar da ƴan wasa ne kuma ya iya tafiyar da ƴan wasa yadda ya kamata—-RONALDO


Shahararren Tsohon ɗan wasan kulob ɗin Real Madrid da ke ƙasar Spain,kuma ɗan asalin ƙasar portugal, Cristiano Ronaldo, a shekaranjiya Laraba ne ya fito fili tare da yaba wa kocin ƙungiyar kwallon kafa ta Real Madrid Zinedine Zidane.
Inda Ya ce a gaskiya Zidane ƙwararren koci ne wanda ya san yadda yake tafiyar da harkar horarwa, wanda hakan ta sa yake samun nasara a hakokin sa na horaswa
Zidane dai ya samu nasarar lashe kofunan zakarun kulob ta nahiyar Turai sau uku a jere amma sai ya yi murabus a farkon kakar wasa ta bana. Daga bisani A watan jiya ya sake karɓar ragamar horar da Madrid bayan mahukuntan ƙungiyar sun lallashe shi.

Ronaldo, wanda ya canza sheƙa zuwa kulob ɗin Juventus dake ƙasar Italiya, kafin ya bar Madrid ya lashe kofin zakarun kulob na Turai sau hudu, sai dai uku daga cikin nasarorin da ya samu, ne a ƙarƙashin horarwar Zidane.


Labarin wasanni
Kungiyar Kwallon Kafa Ta Manchester United Ta Cire Dan Wasanta Anthony Matial A Tawagar Da Za Ta Fafata Wasan Karshe Na Kofin FA


Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta cire dan wasanta Anthony Matial a cikin tawagar da za ta fafata wasan karshe na kufin FA .

Kamar yadda kungiyar ta fitar a jiya Talata ta ce dan wasan Matial ya samu rauni don haka ba zai samu damar bugawa kungiyar wasa ba.
Dan wasan na Faransa wato Anthony Jordan Matial ya na da shekaru 27 sannan ya fafata wasanni kimanin 162 a Manchester United tare da cin kwallaye 62 tun bayan zuwansa Man United daga Manaco shekarar 2015.

Wasan Wanda ake saran fafatawa a ranar Asabar Wanda da kungiyar kwallon kafa ta Manchester City shi ne wasan karshe don daukar kofin FA a kasar Birtaniya.

A makon da yagabata ne ranar Lahadi Man United ta doke Fulham da ci 2-1 a gasar.
Sannan ana saran fafatawar da Man City a ranar Asabar.

Labarin wasanni
Ana Tuhumar Barcelona Da Laifin Bawa Alkalan Wasa Cin Hanci


An tuhumi kungiyar kwallon kafa ta Barcelona dake kasar Sifaniya, bisa zargin bayar da cin hanci ga kungiyar alkalan wasanni, wanda Barcelonan ta musanta.

Ana tuhumar kungiyar ne dai da laifin na bayar da cin haci dangane da wani biyan kudi da suka yi ga Jos Maria Enriquez Negreira, wanda shine tsohon mataimakin shugaban kungiyar alkalan wasannin kasar Sifaniya.
A watan da ya gabata an gano cewa kungiyar ta bawa Negreira da kamfaninsa kudi kimanin Yuro Miliyan 8 da dubu 400, a tsakanin shekarar 2001 zuwa shekarar 2018.

A Juma’ar da ta gabata ne dai aka sanar da kotu a Birnin na Barcelona cewa, kungiyar da tsoffin shugabanni da Negreira ana zargin su da laifin rashawa, karya ka’ida da kuma harkar kasuwancin karya.

Hakan ya faru ne kwanaki Kadan da shugaban na Barcelona Joan Laporta ya karyata cewa, kungiyar tasu ta bawa alkalan Wasanni kudi.

Shugaban gasar Laliga JavierTebas a nasa bangaren yace, Laporta din ya kamata yayi murabus daga mukaminsa tunda ya kasa fito yayi bayanin yaddda musayar kudin ta kasance.
Tun farko dai wani gidan rediyo mai suna Ser Catalunya ne ya fara bayyana cewa, hukumar karbar haraji sun gudanar da bincike akan kamfanin Negreira Dasnil 95.
Labarin wasanni
Ina Da Burin Taka Leda A Gasar Firimiyar Ingila – Osimhen


Dan wasan da ke kan gaba wajen jefa kwallo a gasar Siriya A ta kasar Italiya Victor Osimhen yace, yana mafarkin taka leda a gasar firimiyar kasar Ingila.

Dan wasan gaban kasa Najeriyar wanda ya kasance a Birnin Rum dan karbar kyautar zakakurin dan wasa daga haure, yace yana son kawo Babbar gasa ga Kungiyarsa ta Napoli kuma yana son ya d’an gusa.
“Da yawan mutane suna ganin gasar firimiyar Ingila a matsayin babbar gasa mafi girma a Duniya.” Osimhen ya fada.

Kuma ya kara da cewa “yanzu ina cikin daya daga manyan gasoshi na Duniya, wato Siriya A ta Italiya.”

“Kwarai dagaske ina yin dukkan mai yiwuwa dan cimma buri na na bugawa a gasar Firimiya wata rana, amma komai zuwa yake kuma zan cigaba da kokari” in ji Osimhen.

Osimhen ya koma kungiyar Napoli ne a shekarar 2020, daga kungiyar Lille ta Faransa.
Yanzu haka ya jefa kwallaye 19 a wannan kakar wasannin, kuma kungiyar Napoli ita ke jan ragamar jadawalin gasar da tazarar maki 15.
-
Al'ada4 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare4 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Mu shaƙata4 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Labarai4 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Labarai2 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?
-
Labarai1 year ago
Da Ɗumi-Ɗumi A Na zargin Bam Ya Tashi a Unguwar Sabon Gari A Kano Yanzu