Connect with us

Lafiya

Maza ƴan shekaru 50 sun fi fuskantar cutar kansar Mazakuta

Published

on

Kamar yadda Wani Kwararren likita kuma masani a bangaren magunguna da zamantakewar Iyali mai suna Dakta Ugwele dake Asibitin Tarayya a jihar Abia.
Inda Yace Maza masu Shekaru Hamsin (50) zuwa sama su sukafi fuskantar kamuwa da cutar kansar mafitsara.
Dakta Ugwele ya bayyana hakan ne ga manema labarai.
Kamfanin dillancin labarai ta ƙasa (NAN) ta rawaito cewa Binciken Ugwele ya nuna cewa matsalar kansar mafitsara sananna ce ga maza masu yawan shekaru, kuma mafi yawanci maza da suke sama da shekaru Hamsin (50) na da irin wannan alamar ciwon.
Yace wannan ciwon nada matukar matsala a rayuwa saboda rashin fahimtar ciwon da mutane basuyi ba.
Ya ƙara da cewa rashin fahimtar matsalar ya jawo dubban jama’a rasa rayuka sakamakon rashin baiwa ciwon kula da neman hanyar magance shi.
Dakta Ugwele yace matsalar kansar mafitsara tana bayyana kanta ne ta hanyar kumburan ƴaƴan maraina shine ake kiranshi da kansar Mafitsara.
Dakta Ya ƙara da cewa, Manyan Alamun da ke tattare da Kansar mafitsara sune: Yawan fita Fitsari, Rashin ƙare fitsari gaba ɗaya lokacin yinshi, sannan ɗigan Fitsari lokacin da yake zuwa.
Dakta Ugwele ya bada shawara ga duk wanda yaga irin wannan alamu to ya hanzarta zuwa Asibiti don duba lafiyarsa.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Buhari Ya Sake Roƙo ASUU Su Janye Yajin Aiki

Published

on

Yayin da kungiyar malaman jami’o’i suka shafe akalla watanni bakwai suna yajin aiki shugaba kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci su hakura su janye .

Rahoton da aka samo ya bayyana cewa, Buhari ya bayyana hakan ne a taron bikin karrama Alhaji Muhammadu Indimi, shugaban kamfanin Oriental Energy Resources Ltd a birnin Maiduguri na jihar Borno.

An gudanar da wannan babban taro ne a cikin jami’ar Maiduguri, daya daga cikin manyan makarantun Najeriya da ke garkame sakamakon yajin da ASUU keyi.

Shugaban ya samu wakilcin shugaban ma’aikatansa Alhaji Ibrahim Gambari, wanda ya zanta kan batutuwa da yawa da suka shafi ilimi a Najeriya.

Da yake tuna batun ASUU tare da yin tsokaci a kai, Gambari ya isar da sakon Buhari da cewa

Yana da kyau su ce wani abu game da wannan yajin aikin na ASUU saboda suna karrama Alhaji Indimi wanda aka shirya wa gagarumin biki a yau domin ci gaban ilimi mai inganci da ya kawo ba a kasar nan kadai ba.

A kan haka, yana so ya isar da kiran shugaban kasa Muhammadu Buhari game da ASUU da ta janye yajin aikin da take yi, ta koma aiki.

Abangare guda, Buhari ya ce tuni tattaunawa tsakanin ASUU da gwamnati akeyi, amma duk da haka kungiyar ta ci gaba da bude makarantu.

Ya kuma koka da cewa, bai dace ASUU su ci gaba da ajiye dalibai a gida ba kasancewar abubuwa sun kasa kankama.

A cewarsa, irin wannan tsawaita wa’adin yaji na dakushe ilimi tare da kawo cikas ga ci gaban mutane.

Continue Reading

Labarai

A Shirye Muke Don Sanya Hannu Ga Makashin Hanifa – Ganduje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da a shirin da take domin ganin ta yi adalci ga malamin makarantar nan, Abdulmalik Tanko da aka yankewa hukuncin kisa.

Jaridar The Guardian ta nuna Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje a shirye yake domin ganin an tabbatar da adalci ga masu laifin kisan.

Babban lauyan gwamnatin Kano, Musa Lawan ya bayyana cewa wasu suna tunanin ba za a hukunta wadanda aka samu da laifin kashe Hanifa ba.

A watannin baya ake zargin wasu mutane da laifin hallaka karamar yarinya mai shekara 5. A watan Yuli ne aka tabbatar masu da laifinsu.

A ranar Alhamis, Musa Lawan ya shaidawa mutanen Kano cewa wadanda aka yankewa hukunci za su dandana kudarsu.

Kwamishinan shari’a yake cewa hukumar gidan gyaran hali za ta bayar da shaidar tabbatar da hukunci, wanda zai fito bayan wa’adin daukaka kara.

Akwai kwanaki 90 da doka ta ba wadanda ake kara da nufin su daukaka shari’a idan ba su gamsu da hukuncin da Alkalin kotun tarayya ya zantar ba.

Idan ba a daukaka kara ba, gwamna zai sa hannu, idan kuwa an koma kotu, za a saurari shari’a.

Continue Reading

Labarai

Lassa Ta Hallaka Mutane 158 A Najeriya

Published

on

Ɓera

Akalla mutane 158 cutar zazzabin lasa ta hallaka a jihohi 24 a fadin kasa Najeriya cikin watanni shida na shekarar 2022 da mu je ciki.

Hukumar da ke aikin dakile cutuka masu yaduwa a Najeriya NCDC ita ce ta bayyana haka a jiya Litinin.

Ta ce mutanen da cutar ta kama sun fito ne daga kananan hukumomi 99 na kasar.

Sannan cutar tafi kama yan shekaru 21 zuwa 30 har ma zuwa masu shekara 90.

Hukumar ta ce mutane 158 sun mutu sakamakon cutar Lassa wanda hakan ke nuna karuwar cutar.

Sannan yawan waɗanda aka kara samu da cutar a wannan lokaci ya fi hauhawa a Jihohin Ondo Edo da kuma Filato.

Kuma ba a samu wani ma’akacin lafiya ba daya kamu da cutar kamar yadda aka saba samu a baya ba.

Hukumar NCDC ta ce suna nan suna aiki da ma’akatar national fever lassa multi patner domin kawo karshen cutar a kasa baki daya.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: