Siyasa
Abinda suka yi muka musu, yadda muka ci zaɓe a Gama – Abba Boss


Ɗan siyasar nan a Jihar Kano Muhammad Aminu Adamu wanda ake kira Abba Boss ya bayyana hanyar da suka bi suka ci zaɓe a Kano.

Abba Biss ya bayyana hakan ne cikin shirin Abokin tafiya da ake tattaunawa da shi a Mujallar Matashiya.
Ya ce a lokacin zaɓen gwamna kafin a tafi zagayen cikon giɓi ƴan kwankwansiyya sun fito da mutane da yawansu ma a a hayyacinsu suke ba, hakan ya sa mutanensu shiga shakku wajen bayyana a wajen zaɓen.

Cikin shirin ya bayyana nasararsu da ɗaukar matakin kowa kwamanda ta hanyar zuba dakarunsu don tsare akwatunansu.

Ya ƙara da cewa duk jita jitar da ake yaɗawa cewa an yi riguma a Gama, a cewarsa ko mutum ɗaya bai ga an nunawa yatsa ba.

Abba Boss ya alaƙanta rashin nasarar jam iyyar PDP da hanyar da suka bi wajen zaɓen ƴan takara.
Sannan ya sha alwashin cigaba da ƙoƙari wajen kawowa al ummar jihar Kano ayyukan cigaba ta hanyar miƙa ƙoƙon bararsu ga gwamnan jihar Kano.
Siyasa
Mutanen Ƙwarai Ba Zasu Taɓa Samun Takara Ba A Siyasar Ƙasar Nan – Mu’azu Babangida


Tsohon gwamnan Jihar Neja Dr Mu’azu Babangida Aliyu ya koka game da yadda tsarin zaben kasar ke tafiya a halin yanzu.

Dakta Babangida ya bayyana hakan ne a gurin wani taro da ya halarta a Jihar Kaduna.
Tsohon gwamnan ya bayyana cewa rashin gaskiyar da ake nunawa a lokacin takara hakan na sanyawa mutanen kirki su ware a siyasa.

A cewarsa irin yadda ake tafiya a yanzu, hakan ne zai sanya mutanen kwarai ba za su taba samun takara ba a ƙasar nan.

Mu’azu ya kara da cewa harkar siyasa a kasar ta zama harkar kashewa da neman kudi, a maimakon hidimtawa al’ummar Kasar.

Ya Kara da cewa hakan ne ke sanyawa mutane a kasar ke ganin lamarin ya zamto hanyar samun kudi ga ‘yan takarar.
Siyasa
Ba Iya Yawan Ƙuri’u Ne Ke Sanya Mutum Cin Zaɓe Ba – Alhassan Ado Doguwa


Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa, ya bayyana cewa cin zabe ba yawan kuri’un da aka kada ba ne kawai, harda bin ka’idoji.

Doguwa ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a gidan Talabijin na Channels TV yayin da yake mayar da martani kan cece-kucen da ake tafkawa dangane da zaben 2023 a jihar Kano.
Ya ce zabuka a tsarin dimokuradiyya irin na Najeriya a kodayaushe suna kan tsari da ka’idoji, kuma tsayawa zabe bisa wadannan ka’idoji ne ke sa a samu ‘yanci da gaskiya.

Ya ce, a gare shi idan aka tambaye shi abin da ke faruwa a Kano, abin da ya saba faruwa ne, Kano ta kasance jiha ce mai ci gaba, mai fafutuka ta fuskar siyasa da akida.

Sannan ya kara da cewa ya kamata mutane su san cewa bawai a zabi mutum shike nuna yaci zabe ba har sai ya cika dukkan sharudan da za su saka ya zama shugaba ga al’umma.

Siyasa
Jam’iyyar NNPP Ta Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja


Jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar Kano ta gabatar da zanga-zangarta zuwa Abuja saboda abin da ta kira da ana neman soke nasararta a zaben 2023.

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa shugabannin NNPP sun ce idan har aka karbe gwamnatin Kano daga hannunsu, za a iya haddasa rikici.
A wani jawabi da Ladipo Johnson ya fitar a ranar Laraba, ya yi gargadi cewa wannan rigima za ta iya shafar har sauran kasashe na Afrika.

Shugaban mai binciken kudi ya karanto jawabin da shugaban jam’iyyar NNPP na rikon kwarya, Abba Kawu Ali ya rubuta a ofishin ECOWAS.

NNPP ta kuma yi tattaki zuwa ofishin jakadancin Amurka da na Birtaniyya da babban ofishin kungiyar EU ta tarayyar Turai a garin Abuja.

Shugabannin na NNPP sun ce daga hukuncin kotun sauraron karar zabe da na daukaka kara, ta fito cewa ana so a zalunci mutanen Kano.
Jawabin Abba Kawu Ali ya ce mafi yawan al’umma sun zabi Abba Kabir Yusuf na NNPP a watan Maris, amma ana shirye-shirye domin a tsige shi. Sai dai jam’iyyar ta ce bazatayi watsi da takardun CTC da aka fitar ba.
-
Mu shaƙata10 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Labarai8 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?