“Bayan sun kamamu suka buƙaci mu basu kuɗi sabpda bamu da kuɗi ya sa suka mana fyaɗe.
Wasu daga cikin ƴan sandan sun yi amfani da lefar fiyawata a matsayin ledar kariya wasu kuwa a haka suka yi amfani da mu” Inji ɗaya daga cikinsu.
Ƴan matan dai an kamasu ne yayin da suke cin duniyarsu da tsinke a mabambanran godan rawa da ke babban birnin tarayya Abuja.
Matan da aka kama sun haura 60 daga samamen da ƴan sanda suka kai.
A cewar wata daga cikinsu ta bayyanawa kotu cewar, an yi musu fyaɗen ne a gefen wata makarantar koyon yaƙi a Abuja, ta ce mutum biyu ne suka haike mata sannan kuma suka kaisu caji ofis gar aka kawosu kotu.


