Connect with us

Mu shaƙata

Tun da nake Ban Taɓa yin Zina ba, kuma bazan yi ba da yardar Allah— Nafisa

Published

on

Jarumar Fina finan Hausa ta “Kanywood” NAFISA ABDULLAHI ta kare kanta Kan zargin da mutane ke yiwa Masu Sana’ar Fina finan Hausa cewa Mutanen banza ne.
Nafisa ta kare kanta da cewa ba ruwanta da kudin kowa, Domin basa Burgeta,a cewar ta da kuɗi zasu ruɗeta to da batakai matakin da take a yanzu ba, tsakaninta da mutanen da suke mu’amala sai dai Soyayya ta Gaskiya.
Nafisa ta bayyanawa Mujallar Fina finai ta “Kanywood” Cewar masu kudi da dama ne suke son yin lalata da ita domin su kaita Su baro ta amma taƙi Amincewa,dasu,
Nafisa tace kuɗi basa Ruɗarta har idan banata bane,
Jama’a dai da dama nayiwa Jaruman fina finan hausa Kallon Mutanen banza da suke Gurɓata Tarbiyar Mutane sai dai ba a taru an zama ɗaya ba a cewar Nafisa.
Nafisa Abdullahi ta ƙara da cewa masu nuna maita da naci a kants Sai dai su haƙura, babu wanda zai kusanceta face Mijinta Wannan Shine Alƙawarin da ɗaukar wa kaina.

Click to comment

Leave a Reply

Mu shaƙata

Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?

Published

on

Chiza Dani waƙa ce da ke tashe a kafofin sadarwar zamani wadda matasa maza da mata ke sauraro a kwanakin nan.

Mawaƙi Abdul D. One ya bayyana mana ma’anar kalmar a wata tattaunawa da Mujallar Matashiya.

Ya ce kalmar ya arota ne daga harshen Buzanci yayin da ya yi wata tafiya zuwa jamhuriyar Nijar.

Abdul D. One ya ce tun bayan da ya ga kalmar rubuce a wayar wani abokinsa a Agadez daga wannna lokacin ya dinga bi har sai da ya gano ma’anar waƙar.

A tattaunawar ya tabbatarwa da Mujallar Matashiya cewar bayan gano ma’anar kalmar ashe ta na nufin ‘Daɗina’ wato kalmar masoyi ko masoyiya a harshen Buzanci.

Ya ce kalmar ta yi daidai da sunan soyayya da ake faɗawa masoya mace ko namiji.

A halin yanzu ana shirin ɗaukar bidiyon waƙar da za a fitar da shi ba da daɗewa ba.

Sai dai ya ce babu fim da ake yi a kan waƙar bai sani ba ko nan gaba.

Mawaƙi Abdul D. One wanda waƙoƙinsa ba su fi hamsin ba a cewarsa.

Sai da ya ce a waƙoƙinsa ba wadda ya fi so kamar waƙar Mahaifiya.

Sai wasu kamar Kar Ki Manta Da Ni, Chiza Dani, Ina Sonki da sauransu.

 

Continue Reading

Labarai

Lulu Da Andalu – Sabon Shiri Domin Juya Akalar Kannywood

Published

on

Yayin da ake ci gaba da samar da hanyoyin nishadantar da masu kallo, kamfanin Blue Sound Multimedia ya haska tallan wasan wkaikwayon da ya samar mai suna Lulu Da Andalu.

Sabon shirin wanda ya tara ƙwararrun jarumai maza da mata, da ma sabbin jarumai da ma’aika masu fasaha domin ganin an ƙirƙiri abubuwa masu ƙayatarwa a cikinsa.

Wanda ya shirya shirin TY Shaba ya bayyana cewar sun shirya shirin ne baya bibiyar tarihi tare da nunw jama’a yadda mutane ke alaƙa da aljanu tun a baya.

Yayin da aka shirya taron nuna tallan shirin wanda aka gayyaci manyan ƴan jarida da ƙararru a ɓangaren, wasu daga cikin waɗand su ka kalla sun bayyana shirin a matsayin wani mataki d zai sauya alƙibilar masana’antar fina-finan Hausa.

Wasu daga cikin waɗanda su ka taka rawa a cikin shirin sun bayyana wa masu kallo rawar da su ka taka a ciki tare da tabbatar da cewar shirin zai kayatar fiye da yadda ake tunani.

Sabon shirin  ya samu aikin bayar da umarni daga Kamilu Ɗn Hausa y ace wannan aikin ya  ƙunshi sabbin hnyoyi na zamani wanda za su ƙayatar da masu kallo a ckin sa.

Jarumai da masu bayar da umarni da ma masu shirya fina-finai ne su ka halarci ɗakin nuna fina finai na Pltinium a ranar Juma’a domin kallon tallan shirin.

Continue Reading

Mu shaƙata

Tsawon shekaru 13 waƙoƙi 100 na rera da bakina – D One

Published

on

Mawaƙi Abdul D One ya bayyana cewar ya kwashe shekaru goma sha uku yana waƙa, tun lokacin da ya samu asalin sunan D One a makarantar sakadire.

Yayin zantarwarmu da shi ya ce ya fara rubutun waƙa a shakarar 2007, sannan ya fara shiga ɗakin rera waƙa a shekarar 2009.

Ya rera waƙoƙi guda 100 da bakinsa.

Sai dai mawaƙin ya bayyana cewar ba zai iya tuna waƙar da ya fara rerawa  da bakinsa ba.

Cikin wata tattaunawar da mujallar Matashiya ta yi da shararren mawaƙin nan da ludayinsa ke kan dawo a masana antar fina finan Hausa wato Abdul D One ya ce waƙar Mahaifiya ya fi ƙauna a rayuwarsa.

Mawaƙin ya bayyana dalilinsa na cewar al’umma sun karɓi waƙar suna ƙaunarta kuma hakane ya sa yake matuƙar son waƙar saboda abinda mutane suke so shi yake ƙauna.

Zantawar tamu bata tsaya iya nan ba har sai da mawaƙin ya bayyana cewar ya yi waƙoƙi da sun haura guda ɗari 100 amma a cikinsu guda biyu rak ya fito a cikin faifan bidiyo.

A karo na biyu Abdul D One ya fito a waƙarsa ta Shalele, bayan waƙarsa ta farko da ya fito cikin faifan bidiyo wato Kece Tawa.

Waƙa ta gaba kuwa itace Zainabu Abu, wadda suka rerata tare da ubangidansa wato Umar M Shareef.

Ana sa ran za su fito tare a cikin faifan bidiyon waƙar wadda itace ta uku wanda D One ke fitowa a faifan bidiyo.

Domin masoyansa su kalla hakan ya sa mawaƙin ke wallafa waƙoƙinsa a shafinsa na youtube Abdul D One.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: