Labaran ƙasa
Najeriya bata da wani tarin arziki -Inji Abdullahi Isah

WAI ME YA SA ‘YAN NAJERIYA, su ke karyar cewa kasar su Kasa ce mai tarin arziki ne? -Daga Abdullahi Isah.

Wannan tambaya ce da na dade ina yi amma har yanzu ban samu wani da ya bani hujja da za ta sa in amince cewa NAJERIYA kasa ce da ta ke da dumbin arziki ba.
Idan kana hira da dan kasar nan game da halin da kasar nan ke ciki abu na farko da zai ga ya ma; ‘wallahi ba don shugaban nin mu ba, da yanzu kasar nan ta ci gaba kamar Amurka ko Ingila’ kai da jin wannan zance ga mai hankali kasan maganar bance ce marar tushe.

Idan ka tambayi mai wannan tutiya cewa menene arzikin da kasar nan ke da shi? Kafin ka rufe baki zai baka amsa ‘Man fetur’, shi a zaton sa kasar da ta ke da man fetur’ ta fi kowace Kasa arziki a duniya kuma kamata ya yi ta fi kowace kasa ci gaba a duniya.

Kafin in yi nisa kan wannan batu zan dan koma baya kan wani irin wannan muhawara da mu ka yi da wani bawan Allah a shekarar 2005 lokacin ni kaina ina da karancin shekaru sosai gaskiya to amma na fuskanci wani lamari da masu shekaru da suka fi nawa suka kasa fahimtar haka.
Abinda ya faru bawan Allah nan cewa ya yi NAJERIYA kasa ce da tafi kowace kasa a duniya arziki, dana tambaye shi arzikin me NAJERIYA ta ke da shi da ta fi kowace kasa a duniya; wato bawan Allah nan da ya fusatan kamar ya dakeni waini da nake yaro me nasani shi fa Malamin tattalin arziki ne a daya daga cikin makarantun Sakandire da ke Kano.
‘Ya ci gaba da cewa, Man fetur’ din Najeriya ba don ana sace kudin da shugabanni ke yi ba wallahi da yanzu mun kai Japan’.
Tabbas jama’a da ke wajen kusan duk sun yarda da abinda ya ce saboda hujjar cewa ni yaro ne bansan komai ba kuma shi Malamin Tattalin arziki ne.
Bayan ya gama hayaniyar sa sai nace to ai wannan lamari ne mai sauki shin jimillar nawa Najeriya ta samu wajen sayar da Man fetur’ a shekarar da ta gabata? Da muka bincika sai da ta kai mu ga aikawa da tambaya a gidan rediyon BBC inda bayan mako 2 aka karanta wasikar, aka yi hira da wani jami’in kamfanin NNPC Wanda ya tabbatar da cewa Najeriya ta samu zunzurutun kudi har dala biliyan 20, abin al’ajabi a ranar aka kuma bayyana a wannan gidan rediyo cewa a birnin Mumbai kawai, kasar Indiya ta samu dala biliyan 20 akan harkar ICT.
Wannan amsa da labarin ya kawo karshen tutiyar da ya ke yi kan arziki da kasar ke da shi.
Amma abin takaici har yanzu har gobe matasa na kasar nan da dama da masu ilimi da marasa ilimin suna ci gaba da tutiyar cewa ai kasar su arzikin da ta ke da shi ya wuce gaban wasa.
Allah sarki mai iko, masu fadin wadannan kalamai ba su san cewa idan za ka sayar da arzikin Man fetur’ na Najeriya kaf din sa gaba daya akwai manyan kamfanoni a duniya da ba zai iya sayan maka su ba.
Misali kamfanin Apple darajar kamfanin ya kai dala tiriliyan daya, Wanda adadin tun fara hakar mai a Najeriya a cikin shekara ta alif da dari tara da hamsin kasar nan ba ta sayar da man da ya kai haka ba.
Jama’ar kasa ta sun kasa gane cewa ilimi ne arziki ba albarkatun kasa ba shi ya sa manyan kasashe da suka fi ci gaba irin su Amurka, Ingila, Faransa, Japan, Italiya, Canada, da Jamus duk ilimi ne ya kai su matsayin da suke ta bangaren kere-kere da bincike na kimiyya.
Kasar China da Indiya duk sun dau turbar ci gaba kuma dukkannin su ilimi ne ya kai su.
Idan man fetur shine arziki me ya sa kasashe da dama a afurka kasafin kudin su ya fi na Najeriya? Me ya sa kudaden da suke samu a shekara ya fi wadda Najeriya ta ke samu?
Wannan lokaci ne da ya kamata matasan mu su farga su tashi su nemi ilimi, gwamnatoci kuwa su zage dantse wajen bunkasa bangaren ilimi.
Labaran ƙasa
Mutane Sama Da 7,000 Sun Dawo Najeriya Bayan Tserewa Sakamakon Rikicin Boko Haram

Gwamnatin tarayya a Najeriya ta dawo da mutane 7,790 waɗanda su ka yi gudun hijira sakamakon hare-haren mayakan Boko Haram.

Hadimin gwamnan jihar Borno Dauda Iliya ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar yau a Maiduguri
Ya ce gwamnan jihar Babagana Zulum ne ya jagiranci tawagar gwamnatin tarayya don dawo da mutanen da su ka yi hijira zuwa Najeriya.

Sanarwar ta ce an dawo da mutanen ne daga ƙasar Chadi.

Ministan jin kai. Najeriya Dakta Yusuf Sununu na daga cikin waɗanda su ka je wajen
Sai ministan rage talauci Aliyu Ahmed da babban sakatare a hukumar kula da yan gudun hijira
Rahotanni sun ce mafi yawa daga cikin waɗanda su ka yi gudun hijirar ƴan jihar Borno ne.
A cewar gwamna Zulum, waɗanda aka dawo da su iya wadanda au ja nuna sha’awar dawowa ne.
Gwamnatin tarayya ta nuna jin daɗi bisa yadda ƙasar Chadi ta rungumi yan kasar tsawon shekaru.
Labaran ƙasa
Ƙarin Kuɗin Kira Da Na Data Zai Kai Kaso 30 Zuwa 60 A Najeriya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce akwai yiwuwar ƙara kudin kiran waya da data da aika sakonni da kaso 30 zuwa 60.

Ministan sadarwa na ƙasa Dakta Bosun Tijani ne ya bayyana haka yayin wata ganawa da aka yi da shi a gidan talabiji na Channels.
Ministan ya ce sun karbi rahoto daga masu masana masu zaman kansu kan yadda karin zai kasance

Tun tuni ministan ya yi watsi da bukatar kara kudin da kaso 100 wanda kamfanonin sadarwa su ka bukata.

A cewarsa, za a yi karin kuma ba da jimawa ba amma ba zai kai da kaso 100 ba.
A makon da ya gabata aka fara wani zama da masu ruwa da tsaki kan batun, kuma aka bayar da umarnin nazartar buƙatar haka.
Kamfanonin sadarwa a Najeriya ne dai su ka ce ba za su iya ci gaba da gudanar da ayyukansu ba na tare da sun yi ƙari a kan kudaden kira da data da kuma na aika sakonni ba.
A cewarsu matukar ana buƙatar ingantaccen sadarwa a ƙasa to ya zama wajibi a yi karin kuɗaɗen.
Labaran ƙasa
Babu Ranar Gyara Wutar Lantarkin Arewa – Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce babu ranar daina lalacewar wutar lantarki musamman babban layin da ke kai wuta yankin arewa.

Ministan makamashi Adebayo Adelabu ne ya bayyana haka yayin kare kasafin kudi na shekarar 2025 a gaban kwamitin majalisar dokoki kan makamashi.
Adebayo ya ce sakamakon rashin tsaro ya sa gwamnatin tarayya ba za ta iya tabbatar da ranar daina lalacewar wutar yankin arewa da kuma gyarawa ba.

A cewarsa, babban layin Kaduna zuwa Shiroro zu a Mando shi ne layi na biyu mafi girma da ke kai wutar lantarki arewa, kuma har yanzu ba a gyara ba saboda rashin tsaro.

A sakamakon rashin gyaran ne ya sa sauran layikan ke ci gaba da faduwa.
Ya ce a yanzu za a ci gaba da fuskantar yawan faduwar layukan wutar.
Ministan ya ce hadin gwiwar da su ka yi da ofishin mashawarcin shugaban kasa kan sha’anin tsaro Malam Nuhu Ribadu bai kawo karshen kalubalen da bangaren ke fuskanta ba.
Ministan ya ce su na shirin saka kyamarorin tsaro da fitilu masu amfani da hasken rana a wuraren da hanyoyin layin lantarki ya ketara domin magance matsalar a gaba.
-
Labarai1 year ago
Mafi Karancin Sadaki A Najeriya Ya Koma Dubu 99,241
-
Mu shaƙata2 years ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Labaran ƙetare6 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Al'ada6 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labarai6 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini5 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Lafiya6 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Mata adon gari6 years ago
Sinadarin gyaran gashi – Adon Gari