Shugaban ƙungiyar Mabiya Addinin Kirista   (CAN) A jihar ta kaduna Joseph Hayab ya buƙaci  gwamnan  jihar Nasir EL Rufa’I  da kar ya kuskura ya sa hannu a dokar bada lasisin wa’azi a jihar.

Hayab yace suna nan suna nazari  akan dokar sannan kuma zasu ɗauki matakin shari’a  kan majalisar dokokin  Muddin basu gamsu da dokar ba.

Sai dai anata ɓangaren jama’atul Nasril Islam, tayi maraba  da dokar ta hannun sakatarenta Yusuf  Adamu.

Tun makon da ya gabata ne majalisar jihar kaduna take ƙoƙarin samar da dokar hana yin wa’azi  a jihar  har sai an an bada lasisi  tare da tantance  irin wa’azin da za’ayi.

Leave a Reply

%d bloggers like this: