GWAMNAN jihar kano Abdullahi Umar Ganduje  ya fito da sabbin tsare tsaren harkokin tsaro  a faɗin jihar, ta hanyar amfani da ƴan sandan da kuma sabon tsarin da ake amfani da shi a duniya na amfani da mutane yan sa kai dake masarautu biyar a jihar nan,

Inda ya bayyanatsarin zai taimaka wajen magance matsalar tsaro a faɗin jihar  dam aba Najeriya baki ɗaya.

Cikin wata sanarwar da sakataren ƴada labarai na gwamnan Abba Anwar  ya fitar cewa gwamna Ganduje  ya himmatu wajen magance matsalar tsaro a faɗin jihar.

Gwamnan ya kuma umarci sarakunan jihar guda biyar dasu cigaba da gudanar da taro na wata-wata da  zasu dinga maida hankali kan matsalar tsaro a jihar.

Leave a Reply

%d bloggers like this: