Connect with us

Siyasa

Kowa ya ganni ya san nafi Kwankwaso koshin lafiya -Gen. Dambazau

Published

on

Dambarwar siyasar Kano wadda ‘yan magana ke cewa sai ‘yan Kano na cigaba da daukar sabon salo a lokacin da Gwamna Ganduje ke cigaba da jan ragamar mulkinsa a karo na biyu, inda tsagin jam’iyyar adawa ta PDP da dan takararta Abba Kabir Yusuf ke kalubalantar zaben gwamnan karo na biyu a gaban kotu.

General Idris Bello Dambazau mai ritaya daya ne daga cikin manyan jiga-jigai a tafiyar Kwankwasiyya a baya, biyo bayan juyin juya halin zaben shekarar nan da muke ciki da ta maida su General Dambazau din zuwa gidan siyasar Gandujiyya da ludayinta ke kan dawo.

General Dambazau ya wallafa wata magana a shafinsa na Facebook a daren yau bayan ya saka wani hotonsa a kishingide, kamar yadda kuke gani a hoton dake kasa, inda yake nuna cewa duk wanda ya kalleshi ya san fa hakika yafi tsohon gwamnan Kano jagoran darikar Kwankwasiyya Engr. Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso koshin lafiya.

Mutane da dama ne dai suka bibiyi wannan batu na dambazau suka kuma yi tsokaci akai, shin ko yaya kuke kallon wannan batu?

Click to comment

Leave a Reply

Siyasa

Mutanen Ƙwarai Ba Zasu Taɓa Samun Takara Ba A Siyasar Ƙasar Nan – Mu’azu Babangida

Published

on

Tsohon gwamnan Jihar Neja Dr Mu’azu Babangida Aliyu ya koka game da yadda tsarin zaben kasar ke tafiya a halin yanzu.

Dakta Babangida ya bayyana hakan ne a gurin wani taro da ya halarta a Jihar Kaduna.

Tsohon gwamnan ya bayyana cewa rashin gaskiyar da ake nunawa a lokacin takara hakan na sanyawa mutanen kirki su ware a siyasa.

A cewarsa irin yadda ake tafiya a yanzu, hakan ne zai sanya mutanen kwarai ba za su taba samun takara ba a ƙasar nan.

Mu’azu ya kara da cewa harkar siyasa a kasar ta zama harkar kashewa da neman kudi, a maimakon hidimtawa al’ummar Kasar.

Ya Kara da cewa hakan ne ke sanyawa mutane a kasar ke ganin lamarin ya zamto hanyar samun kudi ga ‘yan takarar.

 

Continue Reading

Siyasa

Ba Iya Yawan Ƙuri’u Ne Ke Sanya Mutum Cin Zaɓe Ba – Alhassan Ado Doguwa

Published

on

Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa, ya bayyana cewa cin zabe ba yawan kuri’un da aka kada ba ne kawai, harda bin ka’idoji.

Doguwa ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a gidan Talabijin na Channels TV yayin da yake mayar da martani kan cece-kucen da ake tafkawa dangane da zaben 2023 a jihar Kano.

Ya ce zabuka a tsarin dimokuradiyya irin na Najeriya a kodayaushe suna kan tsari da ka’idoji, kuma tsayawa zabe bisa wadannan ka’idoji ne ke sa a samu ‘yanci da gaskiya.

Ya ce, a gare shi idan aka tambaye shi abin da ke faruwa a Kano, abin da ya saba faruwa ne, Kano ta kasance jiha ce mai ci gaba, mai fafutuka ta fuskar siyasa da akida.

Sannan ya kara da cewa ya kamata mutane su san cewa bawai a zabi mutum shike nuna yaci zabe ba har sai ya cika dukkan sharudan da za su saka ya zama shugaba ga al’umma.

Continue Reading

Siyasa

Jam’iyyar NNPP Ta Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja

Published

on

Jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar Kano ta gabatar da zanga-zangarta zuwa Abuja saboda abin da ta kira da ana neman soke nasararta a zaben 2023.

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa shugabannin NNPP sun ce idan har aka karbe gwamnatin Kano daga hannunsu, za a iya haddasa rikici.

A wani jawabi da Ladipo Johnson ya fitar a ranar Laraba, ya yi gargadi cewa wannan rigima za ta iya shafar har sauran kasashe na Afrika.

Shugaban mai binciken kudi ya karanto jawabin da shugaban jam’iyyar NNPP na rikon kwarya, Abba Kawu Ali ya rubuta a ofishin ECOWAS.

NNPP ta kuma yi tattaki zuwa ofishin jakadancin Amurka da na Birtaniyya da babban ofishin kungiyar EU ta tarayyar Turai a garin Abuja.

Shugabannin na NNPP sun ce daga hukuncin kotun sauraron karar zabe da na daukaka kara, ta fito cewa ana so a zalunci mutanen Kano.

Jawabin Abba Kawu Ali ya ce mafi yawan al’umma sun zabi Abba Kabir Yusuf na NNPP a watan Maris, amma ana shirye-shirye domin a tsige shi. Sai dai jam’iyyar ta ce bazatayi watsi da takardun CTC da aka fitar ba.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: