Connect with us

Labaran ƙetare

Zamu sa kafar wando da yan hamayya matukar suka cigaba da yunkurin kifar da gwamnati na– MADURO

Published

on

Shugaban kasar Venizuela Nicolas Maduro yayi barazanar saka kafar wando daya da yan hamayyar kasar muddin suka cigaba da barazanar kifar da gwamnatinsa.

Maduro ya bayyana hakan ne ta cikin bayanin da yayi wa Al’ummar kasar ta kafafen yada labarai, inda yace babu shakka zai samar da wani yanayi na juyin juya hali a kasar muddin yan hamayya suka cigaba da matsa masa lamba.

Tun da farko kakakin Nicolas Maduro yayi ikirarin cewa tsoffin jami’an yan sandan kasar da sojojin kasar suna shirin tada Bom a fadar gwamnatin kasar, tare da kwace babbar birnin kasar (Caracas) da kuma wawure kudaden bankin babbar kasar.

Click to comment

Leave a Reply

Labaran ƙetare

Wakilan Ƙasashen Duniya A Fannin Tsaron Sun Kammala Taron Don Shawo Kan Rikicin Ukraine

Published

on

Wakilan kasashen duniya sun yi wani taro na duba hanyoyin kawo karshen rikicin da ke faruwa a Kasar Ukraine.

Masu bayar da shawara kan harkokin tsaro na ƙasashen da kungiyoyin duniya sun kammala taron tattaunawa a Jeddah dangane da abubuwan da ke faruwa a kasar Ukraine.

A ranar Asabar 5th ga watan Agusta wanda aka yi na kasashen duniya 40 da kuma wasu kungiyoyin duniya ne su ka halarta.

Wakilai a zauren Majalisar Dinkin Duniya sunhalarci taron.

Zaman ya gudana ne karkashin jagorancin karamin minista sannan mai bayar da shawara kan harkokin tsaro Dakta Mosaad Bin Mohammad Al-Aiban.

ki

Wadanda su ka halarci taron sun yabawa kasar Saudiyya bisa gayyato mutane sannan ta shirya tare da tsara taron a cikin kasar.

Taron na zuwa ne a wani bangare na sake daura damara tare da cigaba da kuma ƙara kaimi wanda yarima Mohammad Bin Salman Bin Abdulaziz ya aiwatar, kuma masarautar saudiyya ta shiga tsakani tun a watan Maris na shekarar 2022.

Kasashe da kungiyoyin da su ka aike da wakilcin sun hada da, Argentine Australia, Bahrain, Brazil, Bulgaria, Canada Chile, da kuma ƙasar China.

Sauran su ne hadaddiyar daular Comoros, Czech, Denmark, Egypt, Estonia, European Commission, European Council, Finland, Germany, French Republic, India, Indonesia, Japan, Hashemite, Jordan Latvia da kuma Qatar, Korea, South Africa, Lithuania.

Haka kuma akwai Italian, Kuwait, Netherlands, Norway, Poland, Korea, Romania, Turkey, Hadaddiyar daular larabawa, Amuruka, majalisar dinkin duniya da kuma kasar Ukraine.

Mahalarta taron sun gamsu da cigaba da tattaunawa tare da bayyana ra’ayi, domin samar da hanyoyin na dorewar zaman lafiya.

Sannan sun gamsu da yadda aka samar da cigaba a zaman da ya gabata.

Continue Reading

Labaran ƙetare

Alhazan Najeriya 13 Sun Rasa Rayukan Su A Kasar Saudiyya

Published

on

Akalla Alhazan Najeriya 13 ne suka rasa rayukansu a hajjin bana, yayin da mutane 41,632 suka kamu da rashin lafiya a Kasar Saudiyya.

Shugaban likitocin Najeriya mai kula da alhazai Dakta Usman Galadima ne ya bayyana haka a ranar Lahadi a garin Makka.

Usman ya ce sun kula da marasa lafiya 25,772 a filin Arfa yayin da suka kula da mutane 15,680 a Makkah da Madinah kafin ranar Arfa.

Usman ya kara da cewa mutane bakwai da suka fito daga jahohi daban-daban ne suka rasa rayukansu kafin Arfa .

Galadima ya ƙara da cewa mutanen da su ka rasa rayukansu sun fito ne daga Jihohi kamar haka Jihar Kaduna 2 Osun 2 Filato 1 Borno 1 Lagos 1 Yobe 1 Benue 1 sai kuma birnin Tarayya Abuja 1.

Kazalika Dr Usman ya ce suma jiragen yawo sun samu mutane uku da suka rasa rayukansu.

Sannan ya yi kira da a dakatar da hana tsoffi da kuma marasa lafiya zuwa gurin jifan shaidan sakamakon cinkoson da ake fuskanta.

A yayin jawabinsa Kwamishinan Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON Goni Sanda ya ce za su fara jigilar maniyyata zuwa gida Najeriya a ranar 4 ga watan Yulin da muke ciki zuwa ranar 3 ga watan Agusta.

Continue Reading

Labaran ƙetare

Amurka Da Saudiyya Sun Zargi Bangarorin Da Ke Rikici A Sudan Da Watsi Da Sulhu A Tsakaninsu

Published

on

Bayan sake sanya hannu kan yarjejeniyar dakatar da kai wa juna hare-hare a Sudan, an zargi bangarorin da ke rikici a kasar da sake yin watsi da batun sasanci a tsakaninsu.

Kasashen Amurka da Saudiyya, sun ce suna bincike kan bayanan da ke nuna cewa bangarorin kasar Sudan da ke yaki da juna, sun saba yarjejeniyar nan ta tsagaita wuta da suka cimma a baya-bayan nan.

Wannan na zuwa ne yayin da ake kokarin fara aikin samar da agajin jinkai gadan-gadan a Sudan.

Cikin wata sanarwa ta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu da ke kai komon ganin an sasanta rikicin na Sudan, sun ce bangarorin ba su mutunta abin da aka amince da shi na cewa babu batun afka wa juna tun kafin yarjejeniyar ta fara aiki a ranar Litinin.

Kwamitin da ke sa ido kan tsagaita wutar dai, ya fada a jiya Talata cewa a binciken da ya gudanar ya gano yadda aka yi fatali da abun da aka tsaya a kai game da dakatar da kai wa juna hare-haren.

Ƙasar Sudan na fama da rikici tun bayan da aka smau sabani a tsakanin manyan sojojin ƙasar biyu.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: