Ƙasar masar ta tabbatar da sallamar mai horar da ƴan ƙungiyar kwallon kafa ta kasar biyo bayan rashin nasara da ƙasar tayi a hannun ƙungiyar kwallon kafa ta Afrika ta kudu da ci daya mai ban haushi.

Ƙasar masar itace mai karɓar  baƙoncin gasar kwallon kafa ta nahiyar Afrika dake gudana a halin yanzu, sai dai Tuni ƙasar Afrika T Kudu ta fitar da masar din daga gasar  a zagaye na biyu.

Magoya bayan ƙasar  masar dai sun nuna bacin ransu kan rashin nasara da sukayi  a gasar kasancewar sune masu masaukin baƙi.

Sai dai sun nuna goyon bayan su ɗari bisa ɗari  ga ƙungiyar kwallon kafa ta Najeriya  wacce a halin yanzu ta tsallaka zuwa mataki na kusa da kusa dana ƙarshe  wato( quarter final) tun bayan da ta lallasa  ƙasar Kamaru da ci 3-2.

Leave a Reply

%d bloggers like this: