
Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya sake nanata ƙudurin gwamanatinsa na kawar da barace barace da gararambar almajirai akan titian jihar.
Ganduje ya bayyana hakan ne A lokacin da yake karɓar baƙoncin shugaban masu rinjaye a majalisar tarayya kuma ɗan majalisa mai wakiltar Doguwa da Tudunwada Alhassan Ado Doguwa a fadar gwamantin kano.

Gwamnan na cewa sabon ƙudiurinsa na bada ilimi kyauta zai sa dubban yara a dawo dasu makaranta domin samun ingantaccen ilimi, ya kuma ƙara da cewa dole ne a kawo karshen barace barace wanda ko addini bai amince da wulakanta kai ba da sunan bara.

Anasa jawabin Alasan Ado Doguwa yace sun ziyarci gwamanan ne don nuna gamsuwarsa da kuma miƙa godiya ga gudunmawara da ya bayar don tabbatar dashi a matsayin shugaban masu rinjaye.