Daha Muhammad Sadis Dada

Kungiyar kwallon kafa ta kano Pillars ta lashe gasar Kalubale na kasa a karon Farko a Tarihi, Kungiyar ta Samu Nasarar Lashe wannan Gasa bayan kammala Mintina 90 babu wanda ya samu damar zura kwallo, Inda akayi bugun daka kai sai mai tsaron Raga in Pillars suka samu Nasarar zura Kwallye 5 a raga inda Niger Tanerdors suka zura kwallaye 4.
Jim kadan bayan kammalawar na ji tabakin mai horas da kungiyar wato Ibrahim A Jugunu inda ya godewa Allah da wannan Nasara ganin cewa ba’a taba samun Nasarar lashe kofin ba a tatihin kano, Yace wannan Nasara ce ba kadai gare shi ba, Nasara ce ga Daukacin alumar kano dama Arewacin Nigeria

