Labaran ƙasa
Jami’an tsaro sun yi awon gaba da mawallafin jaridar Sahara Reporters


A yau Asabar ne Jami’an tsaron Farin Kaya wato DSS suka je gidan mawallafin jaridar Sahara Reporters da ke yada labaranta a Shafukan yanar gizo gizo, mai Suna Sowore Omoyele.
Sowore ya kasance da takaran shugaban kasa a jam’iyar ACC, a zaben 2019
Rahotanni na nuni da cewa kama mawallafin na da alaka da kiraye-kirayen da akaji yana yi kwanan nan na Neman a yi wa gwamnatin shugaban kasa muhammad Buhari juyin mulki la’akari da yadda tafiyar gwamnatin tasa take na gaza gamsar da Jama’ar Najeriya.
Kafin a cafke shi dai Omoyele Sowore, na shirin jagorantar zanga zangar neman juyin mulki a Najeriya wanda ya bayyana cewa zata gudana a ranar Litinin 5 ga wannan watan na Agustan da muke ciki.
Madogara liberty



Labaran ƙasa
Tafiya Yajin Aiki Ranar Laraba Babu Gudu Babu Ja Da Baya – NLC


Kungiyar kwadago a Najeriya NLC ta ce ba gudu ba ja da baya wajen tafiya yajin aikin da ta tsara a ranar Laraba.

Kungiyar na ci gaba da mayar da hankali wajen hada kan ma’aikata don ganin an tafi yajin aikin nan da kwana biyu masu zuwa.
Matakin hakan ya biyo bayan tashi baram-baram da kungiyar ta yi bayan wani zama da wakilan gwamnatin tarayya a Abuja.

Matsin rayuwa bayan ƙara farashin litar mna fetur na daga dalilai da ya sa kungiyar za ta tafi yajin aikin.

A baya kungiyar ta shirya tafiya yajin aikin sai dai ta janye daga baya bayan sulhu da aka yi da bangaren gwamnatin tarayya.

Daga bisani kotu ta dakatar da kungiyar daga tafiya yajin aikin.
Ma’ajin kungiyar na ƙasa Hakeem Ambali ya shaida yadda gwamnatin ta yi watsi da zama zaman da aka tsara a ranar Juma’a.
A halin yanzu kungiyar na cigaba da samun goyon bayan ma’aikata don tafiya yajin aikin gama gari a ranar Laraba.
Karin albashi da raba tallafi na daga cikin muradun da kungiyar ta saka a zaman da aka yi da farko.
Labaran ƙasa
NNPC Ta Sanar Da Sabon Farashin Man Fetir A Jihohin Najeriya


Kamfanin man fetir na kasa Najeriya NNPC ya sanya sabon farashin da za a dinga sayar da man fetir a kasar, farashin shi ne daga Naira 488 zuwa 555 ma fi kololuwa.

Wannan yana zuwa ne awanni kadan bayan da sabon shugaban kasa Bola Tinubu ya sanar da janye tallafin na man fetir a fadin kasar.
A yau Laraba ne da safe jami’an hukumar ta NNPC suka ya zama, kuma a karshe suka yanke hukuncin cewa farashin man a manya, matsakaita da kananan wuraren sayarwa zai karu.

Kuma sanarwar ta umarcin dukkanin yan kasuwa da su gyara farashin sayar da man fetir din a dukkan jihohin fadin Najeriya.

Kafin yanzu akwai jita-jitar da aka yi ta cewa za a kayyade farashin man nan ba da dadewa ba, an kuma saki sabuwar takardar jadawalin farashin man na mabanbantan yankunan siyasar Najeriya daga hukumomin.

A cikin takardar kuma an umarci dukkan masu kasuwancin man, da rungumi sauyin nan take ba da bata lokaci ba daga yau Laraba 31 ga watan Mayun shekara ta 2023.
Labaran ƙasa
Jami’an NSCDC Sun Kama Mutane 93 Da Ake Zargin Su Da Aikata Laifuka A Kano


Hukumar ba da kariya ga fararen hula ta tabbatar da kame mutum 93 da ake zargi da aikata laifuka tsakanin watan Janairu zuwa Maris na wannan shekara.

Babban kwamandan hukumar na Jihar Kano malam Adamu Salihu shine ya tabbatar da hakan a lokacin zantawarsa da kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a yau juma’a
Adamu ya tabbatar da cewa daga cikin mutanan da hukumar ta kama ta gurfanar da 29 a gaban kotu yayin da ake cigaba da gudanar da bincike akan mutum 57 kafin gurfanar da su a gaban kuliya.
Babban kwamandan ya ba da tabbacin cewar hukumar na cigaba da gudanar da aiki kamar yadda doka ta tanada, na bada kariya ga al’umma.

Adamu Salihu ya kuma bukaci hadin kan al’umma da su zamto masu bawa jami’an tsaro hadin kai tare da bayanai domin a cewarsa al’amarin tsaro ya shafi kowa da kowa ne ba iya jami’an tsaro ba.


-
Mu shaƙata8 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada4 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare4 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai4 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Labarai6 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?
-
Girke girke5 years ago
YADDA AKE LEMON SHINKAFA