Connect with us

Labaran jiha

Hankalin Wasu Al’ummar jihar Katsina ya tashi sakamakon Kashe wani wani mutum da akayi har lahira

Published

on

DAGA RABIU SANUSI KATSINA.

Kisan wani Mutum mai shekaru 45 a jihar katsina ya tada hankalin mazauna anguwar yammawa.

Lamarin ya faru ne a makon daya gabata ne inda al’ummar unguwar yammawa suka tsinci kan su cikin tashin hankali sakamakon kisan wa ni mutum mai suna Alh, Abdullahi lawal da aka fi sani da Alili, wanda wa su da ba’asan kosuwa nene ba suka shiga gidan shi da ke yammawa cikin birnin katsina da misalin karfe 9:00 na dare.

Wnada suke makwabtaka da Alili sun tabbatar wa da wakilin mujallar matashiya cewa kafin rasuwar marigayin matukin motar daukar mai ne, wato tanka.
Haka zalika sun bayyana cewa mutumin a daren da abin yafaru sai da yayi wa dukkan abokanshi bankwana da suke tare daga bisani ya wuce zuwa gidan shi.
Shigar shi gida keda wahala yaran shi sukayi ma shi tarba cikin murna da annashuwa, bayan dan wa ni lokaci ya ce ma matanshi guda biyu ya gaji yana bukatar ya huta, nan ta ke yayi ma su bankwana ya wuce zuwa dakin sa.
Abin da bai sa ni ba ashe bankwana karshe yayi da iyalin na shi,inda cikin dan kankanin lokaci aka sameshi kwance cikin jini.

Wa ni makusancin mamacin ya tabbatar mana da cewa misalin karfe tara na dare makasan suka iske shi har dakin shi yayin da sukayi mashi harbi biyu ga kai da bindiga.
“Na farko dai sun tambayi kudi da wayoyi tare da tambayar ina Alili yake, suka duba cikin gidan daga bisani suka isa dakin shi, yayin da suka fito da shi daga cikin dakin suka kuma harbeshi a kai har sau biyu sukai fice abinsu batare da sun dauki komi ba” inji makwabtan shi.
Daga bisani an samu marigayi Abdullahi kwance cikin jini da harbi biyu daya a goshi sai daya a tsakiyar kan shi, anyi saurin kaishi asibiti amma a na isa aka tabbatar da ya rigamu gidan gaskiya.

Marigayin ya ra su dai yana da mata biyu Hadiza da Jamila sai yara 19 an mai sutura kamar yadda addini ya tanadar a ranar talata da safe.

Mukaddashin jami’in hulda da jama’a na rundunar Yan sandan jihar katsina ASP Anas Gezawa ya bayyana cewa ana cigaba da bincike dan gano Wanda sukayi kisan ko kuma suke da hannu a kisan.
Rundunar Yan sandar jihar Katsina tana kokari don ganin ta gano wayanda sukayi kisan tare da gurfanar dasu a gaban kuliya.

Click to comment

Leave a Reply

Labaran jiha

Hukumar Hisba A Kano Ta Kori Daya Daga Cikin Kwamandojin Ta

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kori daya daga cikin kwamandojin ta, tare da binciken wasu mutane biyar bisa laifin kawo cikas a yaki da lalata da zamantakewa a jihar.

Shugaban hukumar Sheik Aminu Ibrahim Daurawa ya ce an samu kwamandan da aka kora da aikata rashin da’a, yayin da ake ci gaba da binciken sauran wasu mutane biyar.

Ya bayyana cewa jami’in da aka kora ya saba hada kai da mugayen mutane don tafka munanan ayyuka a jihar.

Ya ce, sun kori Mataimakin Sufeto na Hisbah (DSH) tare da bayyana cewa ana neman sa, duk inda aka same shi a kama shi a gurfanar da shi a gaban kuliya.

A cewar sa ya kan hada kai da masu gudanar da otal din don kada hukumar Hisbah ta mamaye otal din nasu a yayin gudanar da ayyukanta.

Daurawa ya kuma musanta zargin cewa jami’anta sun aske gashin wani da ba dan asalin jihar ba da kwalba bayan sun kai farmaki gidan mata masu zaman kansu a jihar.

Wani mai amfani da kafar sadarwa ta Facebook ne ya yi wannan zargin, amma Daurawa ya yi watsi da batun wanda ya alakanta a matsayin masu tada zaune tsaye.

Continue Reading

Labaran jiha

Gwamnatin Tinubu Ta Maida Hankali Ne Kan Abubuwan Da Suka Addabi Kasar-Remi Tinubu

Published

on

Mai dakin shugaban kasa Bola Tinubu Remi Tinubu ta bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta mayar da hankali ne akan gyaran matsalolin da suka addabi Kasar.

Remi ta bayyana haka ne a yayin da ta halarci coci domin yin addu’o’i da kuma bikin cikar Kasar shekaru 63 da samun ‘yancin kai a ranar Lahadi.

Uwar gidan shugaban ta ce mai gidan ta ya tarar da tarin matsaloli masu yawa daga gwamnatin da ya gada.

Remi ta kara da cewa duk da tarin matsalolin da mai gidan ta ya gada, ya kuduri aniyar shawo kan matsalolin da kasar ke fuskanta.

Kazalika ta ce Tinubu zai yi kokari wajen ganin ya gyara dukkan kurakuran da ya tarar a cikin kasar.

Sannan ta ce nan ba da jimawa ba ‘yan Kasar za su dawo cikin walwala da jindadi daga cikin halin matsin da suka tsinci kansu.

Continue Reading

Labaran jiha

Gwamnatin Kano Za Ta Buɗe Cibiyoyin Koyon Sana’o’in Dogaro Da Kai

Published

on

Gwamantin jihar Kano ta ce za ta buɗe cibiyoyin koyon aikin sana’o’in dogaro da kai a jihar.

Sannan gwamnatin jihar Kano ta rage kashi 50 cikin ɗari na rijistar shiga manyan makarantu a jihar.

Ragin ya shafi iya ɗalibai ƴan asalin jihar Kano ne kaɗai.

A wata sanarwa da kwamishinan ilimi mai zurfi a jihar Dakta Yusuf Ibrahim Ƙofar Mata ya sanyawa hannu, sanarwar ta ce an yanke hukuncin ne yayin wata ganawa da da gwamnan ya yi da shugabannin manyan makarantu a jihar.

Sanarwar ta ce an yi haka ne domin baiwa ɗalibai a jihar damar samun ilimi.

Haka kuma gwamnatin za ta buɗe cibiyoyin koyon sana’o’in dogaro da kai a jihar yadda matasa za su tsaya da ƙafarsu.

Gwamnatin ta ce ta na mayar da hankali domin bayar da ingantaccen ilimi domin cigaban jihar.

Dukkanin ɗalibai da ke karatu a kwalejiji da jami’o’i mallakin jihar Kano kuma su ka kasance yan asalin jihar za su amfana da ragin kudin.

Bai wa ɓangaren ilimi muhimmanci na dga manufofin Injiniya Abba Kabir Yusuf wanda ya sha alwashin haka tun lokacin yakin neman zaben sa.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: