Labaran jiha
Hankalin Wasu Al’ummar jihar Katsina ya tashi sakamakon Kashe wani wani mutum da akayi har lahira

DAGA RABIU SANUSI KATSINA.

Kisan wani Mutum mai shekaru 45 a jihar katsina ya tada hankalin mazauna anguwar yammawa.
Lamarin ya faru ne a makon daya gabata ne inda al’ummar unguwar yammawa suka tsinci kan su cikin tashin hankali sakamakon kisan wa ni mutum mai suna Alh, Abdullahi lawal da aka fi sani da Alili, wanda wa su da ba’asan kosuwa nene ba suka shiga gidan shi da ke yammawa cikin birnin katsina da misalin karfe 9:00 na dare.

Wnada suke makwabtaka da Alili sun tabbatar wa da wakilin mujallar matashiya cewa kafin rasuwar marigayin matukin motar daukar mai ne, wato tanka.
Haka zalika sun bayyana cewa mutumin a daren da abin yafaru sai da yayi wa dukkan abokanshi bankwana da suke tare daga bisani ya wuce zuwa gidan shi.
Shigar shi gida keda wahala yaran shi sukayi ma shi tarba cikin murna da annashuwa, bayan dan wa ni lokaci ya ce ma matanshi guda biyu ya gaji yana bukatar ya huta, nan ta ke yayi ma su bankwana ya wuce zuwa dakin sa.
Abin da bai sa ni ba ashe bankwana karshe yayi da iyalin na shi,inda cikin dan kankanin lokaci aka sameshi kwance cikin jini.

Wa ni makusancin mamacin ya tabbatar mana da cewa misalin karfe tara na dare makasan suka iske shi har dakin shi yayin da sukayi mashi harbi biyu ga kai da bindiga.
“Na farko dai sun tambayi kudi da wayoyi tare da tambayar ina Alili yake, suka duba cikin gidan daga bisani suka isa dakin shi, yayin da suka fito da shi daga cikin dakin suka kuma harbeshi a kai har sau biyu sukai fice abinsu batare da sun dauki komi ba” inji makwabtan shi.
Daga bisani an samu marigayi Abdullahi kwance cikin jini da harbi biyu daya a goshi sai daya a tsakiyar kan shi, anyi saurin kaishi asibiti amma a na isa aka tabbatar da ya rigamu gidan gaskiya.
Marigayin ya ra su dai yana da mata biyu Hadiza da Jamila sai yara 19 an mai sutura kamar yadda addini ya tanadar a ranar talata da safe.
Mukaddashin jami’in hulda da jama’a na rundunar Yan sandan jihar katsina ASP Anas Gezawa ya bayyana cewa ana cigaba da bincike dan gano Wanda sukayi kisan ko kuma suke da hannu a kisan.
Rundunar Yan sandar jihar Katsina tana kokari don ganin ta gano wayanda sukayi kisan tare da gurfanar dasu a gaban kuliya.
Labaran jiha
Sarkin Musulmi Ya Nada Gwamna Nasir Na Kebbi A Matsayin Gwarzon Daular Usmaniyya

Mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na lll ya nada gwamnan Jihar Kebbi Nasir Idris a sarautar gwarzon daular Usmaniyya.

Wakilin Sarkin Musulmi kuma sarkin Argungun Alhaji Samaila Muhammed Mera ne ya mika takardar nadin ga gwamnan a gidan gwamnatin Jihar ta Kebbi a jiya Juma’a.


Alhaji Sa’ad ya nada gwamna Nasir ne a sarautar ta Gwarzon Daular Usmaniyya ne bisa gudummuwar da yake bayarwa na taimakon al’ummar kasar.
Sarkin Muslumin ya bayyana cewa sarautar gwarzon daular Usmaniyya ana bayar da ita ne ga dukkan wanda ya sadaukar da kansa wajen taimakon al’ummar Jiharsa da dama Kasarsa baki daya.
Sarkin na Argungu ya kara da cewa masarautar Sarkin Musulmi na sa ne da irin gudummawa taimako da kuma kyautatawar da gwamnan ya ke bayarwa a wajen inganta rayuwar al’umma.
Acewar Argungun Majalisar masarautar sarkin Musulmi za ta bayyana ranar da za ta nadawa gwamnan rawanin sarautar nan ba da dadewa ba.
A yayin karbar takardar nadin gwamna Nasir ya mika godiyarsa ga masarautar sarkin Musulmi bisa dacewar da ta gani ta nadashi a matsayin.
Sannan gwamna Nasir ya ce gwamnatinsa da mutanen Jihar za su samar da lokaci domin zuwa yin godiya fadar Sarkin Musulmin da ke Jihar Sokoto domin nuna farin cikinsu da nadin da aka yi masa.
Labaran jiha
Gwamnan Legas Ya Yiwa Fursunoni Afuwa

Gwamnan Jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, ya bayar da umarni sakin fursunoni 55 daga gidajen gyaran hali daban-daban na fadin jihar.

Kwamishinam shari’a na jihar, Lawal Pedro, SAN, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rattaɓawa hannu.
Gwamna ya amince da sakin mazauna gidan gyaran halin ne bisa shawarwarin da majalisar duba yiwuwar yiwa fursunoni afuwa ta jihar.


Labaran jiha
Babu Batun Rikici Tsakanin Kwankwaso Da Abba – Gwamnatin Kano

Wasu rahotannin na nuni da cewa, bayan ci gaba da fuskantar rikice-riciken cikin gida da ake ci gaba da fuskanta a jam’iyyar NNPP a Kano, gwamnan Jihar, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya daina daga Wayar uban gidansa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Rahotanni sun bayyana cewa daga cikin abubuwa da suka kara rura wutar rikicin jam’iyyar ciki harda batun nada Kwamishinoni.
Hakan ya sanya gwamna Abba Kabir ya gujewa haduwa da jagoran nasa Rabi u Kwankwaso.

Sai dai bayan bullar takun sakar da ya fara shiga tsakanin Kwankwaso da Abba, gwamnatin Jihar ta Kano ta fito ta musantan jita-jitar da ke yawo cewa baraka ta kunno kai tsakanin gwamnan Jihar Injiniya Abba Kabir Yusuf da ubangidansa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, har ta kai ga baya daga wayarsa.

Hadimin gwamnan na musamman kan shafukan sada zumunta Salisu Yahya Hotoro ne ya bayyana hakan ta cikin wata wallafa da yayi a shafinsa na facebook a yau Litinin.
Hadimin gwamnan ya bayyana cewa ko kadan babu kanshin gaskiya a cikin rahotannin da ake yadawa akan Kwakwaso da Abba.
Acewar Hotoro har yanzu akwai alaka mai karfi tsakanin Kwankwaso da Abba, babu wani abu da ta shiga tsakaninsu.
Gwamnatin ta Kano ta bukaci mutane da su yi watsi da jita-jitar da ba ta da tushe balle makama.
-
Labarai1 year ago
Mafi Karancin Sadaki A Najeriya Ya Koma Dubu 99,241
-
Mu shaƙata2 years ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Labaran ƙetare6 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Al'ada6 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labarai6 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini5 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Lafiya6 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Mata adon gari6 years ago
Sinadarin gyaran gashi – Adon Gari