Manoma kaji a jIhar Kano sun sha alwashin ɗaukar mataki muddin gwamnati ta ƙi magance matsalar da suke fuskanta.

Alhaji Muhammadu Aminu Adamu wanda mutane suka sani da Abba Boss ne ya bayyana hakan cikin wani shiri da aka yi da shi a mujallar Matashiya.

Abba Boss wanda shi ne shugaban kamfanin NANA FARM LTD ya ce akwai kamfanin da gwamnati ta bawa dama don yin sana a irin tasu alhali hakan zai zamto barazana ga masu ƙaramin ƙarfi.

“Hakan babbar illa ce kuma mabaraza ce ga tsaro duba ga mutanen da suke ta barin sana ar saboda ƙarancin kasuwa” Inji Abba Boss.

Ya ce kamfanin na ƙyan,ƙyasar kaji ya siyar musu daga baya kuma ya zo yana yin kwai sannan su siyar a farashi ƙasa da nasu kuma hakan ya saɓa ga dokar ƙasa.

Sannan ya yi kira dababbar Murya cewa ya kamata gwamnati ta ɗauki mataki in kuma ba haka ba su da kansu za su ɗauki mataki.

“Da yawan manoma kaji na barin sana ar tasu saboda rashin ciniki da suke fuskanta”. Abba Boss.

Leave a Reply

%d bloggers like this: