Connect with us

Labarai

Muna da karancin masu kishi a Arewa -Nasiru Zango

Published

on

Arewa da sauran gyara?
Babbar matsalar mu a Arewa shine rashin hadin Kai da rashin kishin junan mu, sai kuma matsalar aikin yi wacce ke Sawa matasan yankin, na yin ayari su nufi kudancin kasar domin ci rani, a wajen ci ranin ne suke gamuwa da wulakanci, kwatankwacin Wanda ya faru GA matasan Arewa su 123 a Ikko. Wannan abin haushi ne Wanda ke nuna cewar al’ummar Arewa sun zama saniyar ware, jagororin mu kuma Galibinsu idon su ya rufe basa hango komai sai abin da zasu samu su tarawa iyalansu dukiya. Muna gani kirkiri matasan mu na gararamba a Gari Amma an kasa hada Kai domin tunanin tartibiyar hanyar samar da makoma ga yankin. Wani abu dake damu na, shine duk da cewar matasan Arewa sune, suka fi yawa amma duk wani gurbin aiki da aka samu na bankuna, Kamfanoni masu Zaman kansu, ko kantunan zamani, sai ka iske ba matasan Arewa ake baiwa gurbin ba, alal misali, duk da yawan namu, kiri kiri za a samu gurbin aiki a Kano ko katsina, Amma idan kaje kaga ma aikatan sai kayi ta mamakin yadda aka dauki aikin domin yawanci wadanda ake baiwa ayyukan ba Yan Arewa bane, kaga kenan can sun cike nasu guraben ayyukan, na Arewan ma sunzo sun cike ko kuma an cike dasu. Wai meye matsalar ne? Hatta aikin gadi a manyan kantunan zamani (shopping malls) indai na Yan kasashen waje ne, zaka tarar mutanen Arewa kalilan ne, to shin matasan mu ne basa aikin ko kuwa jagororin mu ne basu da kishin mu? Nasan dai ko aikin gadi aka samu a yanzu a Kano ko katsina da sauran su akwai dimbin matasan mu da zasu yi rige rigen karba, domin nasan matasan dake da digiri da diploma ko NCE da suka yi karatun zama masu gadi kuma suke aikin gadin a yanzu,amma zai yi wuya ka gansu a irin wadannan wurare suna gadin, to Wai meye laifin su? Wani abu da nake mamakin sa shine yadda abin ya Sha bambam a kudancin Nigeria, domin zai yi wuya a Bude shop rite ko Grand square da sauran irinsu a Lagos ko Enugu kuma kaga Galiban ma’aikatansu mutanen Arewa ne,sai dai a Arewa, saboda muna da Karancin masu kishi wadanda zasu tsaya tsayin daka domin ganin an yi adalci kowa an bashi hakkin sa, Da zamu yi, yadda ake a kudu da watakila mun rage yawan matasa masu gararamba a Gari, Yawanci wakilan mu da jagororin mu, sun fi son fafa, da birgewa kaga mutum Dan tsigigi bashi da ko dubu 50 cikakkiya Amma da an zabe shi ya samu dama sai kaga yana ta sayen gidaje a GRA da manyan motoci ya sauya mu’amilla yayi ta sharholiya domin a zatonsa ya Sha kwana, Ya manta da irin wadannan matasa wadanda watakila ma sune suka taimaka wajen tsare masa akwatu.Ya kamata mu farka mu gane cewar zamani fa sauyawa yake, Kuma baka da inda yafi yankin ka, idan takamar ka, ka riga kasha kwana ne, to fa akwai sauran aiki a gaba. Allah ya maganta mana, ya saita mana shugabannin mu ya saita su akan hanyar daidai. Allah ya kawo mana tallafi ya ceto mu daga fadawa ramin da muke tunkara.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Yan Sanda A Osun Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Mahaifiyarsa

Published

on

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mutum mai suna Lukman Adejoju bisa zargin kashe mahaifiyarsa dattijuwa mai suna Aminat.

 

Jaridar Punch ta ruwaito a ranar Lahadi, 14 ga watan Afrilu cewa Lukman, mazaunin kauyen Kajola ne da ke kusa da Apomu a jihar Osun.

 

Rahoton ya bayyana cewa mutumin ya kashe mahaifiyarsa, wadda aka ce tana da shekaru kusan 100 a duniya, sakamakon takaddamar da ta shiga tsakaninsu kan manja.

 

Wani ganau mai suna Rasaki ya bayyana a ranar Lahadi cewa Lukman da mamaciyar sun dauki wani lebura ne wanda ya taimaka musu wajen siyar da wasu jarakunan manja.

 

Yayin da leburan ya dawo masu da kudin, an ruwaito marigayiya Aminat ta dage cewa sai dai a ba ta kudin, lamarin da ya harzuka dan nata Lukman.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

DSS Sun Kama Ta Hannun Damar Nasir El-Rufai

Published

on

Jami’an hukumar DSS sun kama wata ƴar siyasa ta jam’iyyar APC, Aisha Galadima, a jihar Kaduna.

 

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an kama ƴar siyasar wacce ta hannun daman tsohon gwamnan jihar, Nasir Ahmad El-Rufai ce a ranar Lahadi, 14 ga watan Afirilun 2024.

 

Rahoton ya nuna cewa kamun da aka yi mata na da nasaba da wani rubutu da ta yi a soshiyal midiya kan gwamnan jihar Malam Uba Sani.

 

A cewar majiyoyi, Aisha Galadima ta caccaki Gwamna Uba Sani bisa kalaman da ya yi kan Nasir El-Rufai, a shafinta na Facebook.

 

Wani maƙwabcinta ya bayyana cewa an kamata ne a gidanta da ke unguwar Tudun Wada a Kaduna a ranar Lahadi, yayin da wata ƙawarta ta ce an kashe wayoyinta bayan kamun da aka yi mata.

 

Sai dai, babban sakataren yaɗa labarai na gwamnan Kaduna, Muhammad Lawal Shehu, ya ce bai da masaniya kan kamun da aka yi mata.

 

Shehu ya yi nuni da cewa a tuntuɓi hukumar tsaron farin kaya ta DSS domin samun ƙarin bayani kan lamarin.

Kuma har kawo wannan lokaci, hukumar ba ta ce komai dangane da kamun da ta yi wa matar ba.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

EFCC Ta Kwato Biliyan 32.7 Da Aka Wuwure A Ma’aikatar Jin-kai

Published

on

Hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa a Najeriya EFCC ta ce ta ƙwato Naira biliyan 32.7 da $445,000 da ake zargin wawushe a ma’aikatar jin ƙai da yaƙi da fatara.

 

Hukumar ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa a shafin X da kakakinta, Dele Oyewale, ya fitar a ranar Lahadi, 14 ga watan Afirilun 2024.

 

EFCC ta bayyana hakan ne bayan abin da ta kira yadda ake ta yawan maganganu kan binciken da take yi a ma’aikatar jin ƙai da yaƙi da fatara.

 

Oyewale ya yi bayanin cewa a farkon binciken da hukumar ta fara, ta gayyato tsofaffi da dakatattun jami’an ma’aikatar domin jin daga bakinsu.

 

A cewar kakakin na EFCC, hukumar ta kuma fara binciken wasu ayyukan zamba da suka haɗa bashin da aka ciyo daga bankin duniya, kuɗaɗen Covid-19 da kuɗaɗen da aka karɓo na Abacha waɗanda aka ba ma’aikatar domin rage raɗaɗin talauci.

 

A farkon fara bincike, an gayyato tsofaffi da dakatattun jami’an ma’aikatar jinƙai, kuma binciken da ake yi kan zargin zamba ya sanya ya zuwa yanzu an ƙwato N32.7bn da $445,000.

 

Binciken kuma ya bankaɗo jami’an ma’aikatar masu yawa waɗanda ake zargin da hannunsu wajen yin sama da faɗi da kuɗaɗen.

 

Rundunar yan sandan a jihar Osun sun kama wani maidanci bisa laifin kashe mahaifiyarsa.

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: