Connect with us

Siyasa

Siyasar Kano: Yau Shekara Daya da Komawar Shekarau APC

Published

on

Yau Shekara Daya da Komawar Shekarau APC

 

Malam Dr. Ibrahim Shekarau wanda tsoho malamin makranta ne wanda yayi gwamna har hawa biyu, wato tsawon shekaru takwas a Kano, karkashin jam’iyyar ANPP, Mallam Shekarau ya zama gwamna karo na farko a shekarar 2003 bayan da ya kada gwamna mai mulki Engr. Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso, wanda kuma Engr. Kwankwaso ya kara karbar mulki daga hannun Mallam Shekarau bayan da ya kammala zangon mulkinsa na biyu, ya kuma tsayar da danle lensa a takara wato Malam Salihu Sagir Takai.

Tsawon wannan lokaci ana ta tafka adawa kala-kala tsakanin manyan gidajen siyasar Kano wato gidan Mallam Shekarau da kuma gidan Engr. Kwankwaso.

Juyin juya halin siyasa da aka samar musamman na hadin kan jam’iyyun adawa wanda aka faro daga jam’iyyar CPC har zuwa APC mai lakabin MAJA wadda shugaban kasa na yanzu Mallam Muhammadu Buhari ya jagoranta sai ta sanya Mallam Shekarau ya tsinci kansa a jam’iyyar APC wanda ya zamo daya daga cikin manyan jiga-jigai da suka kafa jam’iyyar.

Sai dai a ranar wata Laraba ta watan Janairu na shekarar 2014 lokacin da zaben shekara ta 2015 ke kara karatowa Mallam Shekarau ya yanke shawarar barin jam’iyyar APC inda ya koma jam’iyyar PDP, wadda ake kallon hakan ya biyo bayan kome da Engr. Kwankwaso yayi zuwa jam’iyyar da su Shekarau suka kafa wato APC kuma ya shigo da gwamnati sukutum wanda hakan ya sanya ya kwacewa Mallam Shekarau madafun iko a jam’iyyar.

Shugaban kasa a wancan lokaci Good luck Jonathan ya karbi Mallam Shekarau hannu bibiyu harma ya bashi mukamin ministan ilimi na tarayyar Nigeria.

Kwankwaso ya cigaba da jagorantar jam’iyyar APC a Kano inda shima ya tsayar da mataimakinsa Dr. Abdullahi Umar Ganduje a matsayin dan takarar gwamna a zaben shekarar 2015 a yayinda shi kuma Malam Shekarau ya kara tsayar da Mallam Salihu Sagir Takai a jam’iyyar PDP.

 

Jam’iyyar APC ita ta lashe wannan zabe na 2015 daga gwamna har zuwa shugaban kasa, inda shi kuma Kwankwaso ya nemi Sanata mai wakiltar Kano ta tsakiya kuma yayi nasara a zaben, haka aka yi tafiya.

 

Rigima ta barke tsakanin Kwankwaso da kuma gwamna mai mulki Ganduje wadda har ta tilastawa Kwankwaso ficewa daga jam’iyyar APC inda ya sake komawa jam’iyyarsa ta asali wato PDP, inda aka kara mai-maita irin abinda ya faru a APC a 2014 inda Kwankwaso ya kara kwace madafun ikon jam’iyya daga hannun Mallam Shekarau, hakan kuwa shine ya sake tilastawa Mallam Shekarau din ya bar jam’iyyar ya dawo jam’iyya mai mulki ta APC a irin wannan rana ta 4 ga Satumban shekarar 2018, inda ya hada kai da gwamna mai ci Ganduje.

 

Jam’iyyar APC a Kano ta tsayar da Mallam Shekarau matsayin sanata mai wakiltar Kano ta tsakiya wato mukamin da Engr. Kwankwaso ke kai a wancan lokacin, inda a gefe guda gwamna Ganduje ya sake neman zagaye na biyu, Kwankwaso kuma ya tsayar da Abba Kabir Yusuf a matsayin dan takarar gwamna.

A wannan zabe Shekarau ya lashe kujerar sanata wadda yake kai a yanzu, Ganduje ya koma kujerar gwamna, wadda har yanzu ake gaban kotu tsakaninsu da tsagin Kwankwaso wanda basu gamsu da sakamakon zaben ba.

Wannan sune kadan daga wasu batutuwa da suka faru a siyasar Kano wadda hausawa ke cewa sai Kano.

Sharhi: Basheer Sharfadi

Click to comment

Leave a Reply

Siyasa

Mutanen Ƙwarai Ba Zasu Taɓa Samun Takara Ba A Siyasar Ƙasar Nan – Mu’azu Babangida

Published

on

Tsohon gwamnan Jihar Neja Dr Mu’azu Babangida Aliyu ya koka game da yadda tsarin zaben kasar ke tafiya a halin yanzu.

Dakta Babangida ya bayyana hakan ne a gurin wani taro da ya halarta a Jihar Kaduna.

Tsohon gwamnan ya bayyana cewa rashin gaskiyar da ake nunawa a lokacin takara hakan na sanyawa mutanen kirki su ware a siyasa.

A cewarsa irin yadda ake tafiya a yanzu, hakan ne zai sanya mutanen kwarai ba za su taba samun takara ba a ƙasar nan.

Mu’azu ya kara da cewa harkar siyasa a kasar ta zama harkar kashewa da neman kudi, a maimakon hidimtawa al’ummar Kasar.

Ya Kara da cewa hakan ne ke sanyawa mutane a kasar ke ganin lamarin ya zamto hanyar samun kudi ga ‘yan takarar.

 

Continue Reading

Siyasa

Ba Iya Yawan Ƙuri’u Ne Ke Sanya Mutum Cin Zaɓe Ba – Alhassan Ado Doguwa

Published

on

Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa, ya bayyana cewa cin zabe ba yawan kuri’un da aka kada ba ne kawai, harda bin ka’idoji.

Doguwa ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a gidan Talabijin na Channels TV yayin da yake mayar da martani kan cece-kucen da ake tafkawa dangane da zaben 2023 a jihar Kano.

Ya ce zabuka a tsarin dimokuradiyya irin na Najeriya a kodayaushe suna kan tsari da ka’idoji, kuma tsayawa zabe bisa wadannan ka’idoji ne ke sa a samu ‘yanci da gaskiya.

Ya ce, a gare shi idan aka tambaye shi abin da ke faruwa a Kano, abin da ya saba faruwa ne, Kano ta kasance jiha ce mai ci gaba, mai fafutuka ta fuskar siyasa da akida.

Sannan ya kara da cewa ya kamata mutane su san cewa bawai a zabi mutum shike nuna yaci zabe ba har sai ya cika dukkan sharudan da za su saka ya zama shugaba ga al’umma.

Continue Reading

Siyasa

Jam’iyyar NNPP Ta Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja

Published

on

Jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar Kano ta gabatar da zanga-zangarta zuwa Abuja saboda abin da ta kira da ana neman soke nasararta a zaben 2023.

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa shugabannin NNPP sun ce idan har aka karbe gwamnatin Kano daga hannunsu, za a iya haddasa rikici.

A wani jawabi da Ladipo Johnson ya fitar a ranar Laraba, ya yi gargadi cewa wannan rigima za ta iya shafar har sauran kasashe na Afrika.

Shugaban mai binciken kudi ya karanto jawabin da shugaban jam’iyyar NNPP na rikon kwarya, Abba Kawu Ali ya rubuta a ofishin ECOWAS.

NNPP ta kuma yi tattaki zuwa ofishin jakadancin Amurka da na Birtaniyya da babban ofishin kungiyar EU ta tarayyar Turai a garin Abuja.

Shugabannin na NNPP sun ce daga hukuncin kotun sauraron karar zabe da na daukaka kara, ta fito cewa ana so a zalunci mutanen Kano.

Jawabin Abba Kawu Ali ya ce mafi yawan al’umma sun zabi Abba Kabir Yusuf na NNPP a watan Maris, amma ana shirye-shirye domin a tsige shi. Sai dai jam’iyyar ta ce bazatayi watsi da takardun CTC da aka fitar ba.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: