Kwamishinan ƴan sandan jihar Kano kuma mataimakin sufeton ƴan sandan Najeriya Ahmed Iliyasu ne ya bayyana hakan.

Ya ce an ceto yro ɗaya a jijar Anambara wanda kuma yanzu haka yara goma aka kuɓutar cikin 47 da ake zargi an siyar da su a jihar.

Kamar yadda muka baku labari a baya, rundunar ƴan sandan jihar Kano ce ta fara aikin bankaɗo asirin mutanen da ke sace yara ƙanana da shekarunsu ba su haura goma ba.

Ana siyar da yaran ne don bautar da su tare da sauya musu addini, da farko dai an ceto yara tara bayan nan kuma aka sake ceto yaro ɗaya wanda aka sace daga Kano zuwa Anambara.

Leave a Reply

%d bloggers like this: