Connect with us

Labaran jiha

Gwamnatin Kano na cigaba samar da gidajen siyarwa a farashi mai rahusa

Published

on

Kwamishinan Maaikatar Gidaje da Sufuri Barrister Musa Abdullahi Lawal ya bayyana shirin Gwamnatin Jihar Kano na ci gaba da samar da rukunin gidaje a farashi masu rahusa da yan Asalin Jihar zasu mallaka cikin sauki.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi ragamar aikin maaikatar sufuri da gidaje ta jihar Kano.

Ya tabbatar da cewar sake samar da rukunin gidaje a sassan jihar zai tallafa don magance matsalolin da karancin gidaje ke haifarwa a jihar, inda yace jihar kano tana bukatar sake gina rukunin gidaje duba da yadda jihar ke sake habaka ta fannin yawan alumma.

Kwamishinan maaikatar sufuri da gidaje ya kuma sake bayyana cewar gwamnatin Jihar kano za ta samar da ingantaccen shirin don tsabtace masu sana,ar babura masu kafa uku, yace gwamnati zata yi haka ne ta hanyoyin samar da ingantaccen tsari na yiwa masu baburan rijista domin yin duba akan ayyukansu da kuma zirga zirgarsu.

Ya kuma ce gwamnati zata Samar da tsarin zirga zirgar motocin haya na bai daya domin kamar yadda yake a sauran kasashen duniya da suka ci gaba

Barrister Musa Abdullahi Ya kuma yi kira ga maaikatan Hukumar da su mara masa baya domin samun nasarorin da yake fata tare da ciyar da gwamnatin jihar kano a fannin sufuri da gidaje.

Kwamishina Musa Abdullahi Ya kuma gargadi maaikatan maaikatar da su guji makara da fashi ba tare wani kwakwran uzuri ba.
Ya kuma hore su da su kauracewa sabawa dokokin maaikatan jihar

Click to comment

Leave a Reply

Labaran jiha

Hukumar Hisba A Kano Ta Kori Daya Daga Cikin Kwamandojin Ta

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kori daya daga cikin kwamandojin ta, tare da binciken wasu mutane biyar bisa laifin kawo cikas a yaki da lalata da zamantakewa a jihar.

Shugaban hukumar Sheik Aminu Ibrahim Daurawa ya ce an samu kwamandan da aka kora da aikata rashin da’a, yayin da ake ci gaba da binciken sauran wasu mutane biyar.

Ya bayyana cewa jami’in da aka kora ya saba hada kai da mugayen mutane don tafka munanan ayyuka a jihar.

Ya ce, sun kori Mataimakin Sufeto na Hisbah (DSH) tare da bayyana cewa ana neman sa, duk inda aka same shi a kama shi a gurfanar da shi a gaban kuliya.

A cewar sa ya kan hada kai da masu gudanar da otal din don kada hukumar Hisbah ta mamaye otal din nasu a yayin gudanar da ayyukanta.

Daurawa ya kuma musanta zargin cewa jami’anta sun aske gashin wani da ba dan asalin jihar ba da kwalba bayan sun kai farmaki gidan mata masu zaman kansu a jihar.

Wani mai amfani da kafar sadarwa ta Facebook ne ya yi wannan zargin, amma Daurawa ya yi watsi da batun wanda ya alakanta a matsayin masu tada zaune tsaye.

Continue Reading

Labaran jiha

Gwamnatin Tinubu Ta Maida Hankali Ne Kan Abubuwan Da Suka Addabi Kasar-Remi Tinubu

Published

on

Mai dakin shugaban kasa Bola Tinubu Remi Tinubu ta bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta mayar da hankali ne akan gyaran matsalolin da suka addabi Kasar.

Remi ta bayyana haka ne a yayin da ta halarci coci domin yin addu’o’i da kuma bikin cikar Kasar shekaru 63 da samun ‘yancin kai a ranar Lahadi.

Uwar gidan shugaban ta ce mai gidan ta ya tarar da tarin matsaloli masu yawa daga gwamnatin da ya gada.

Remi ta kara da cewa duk da tarin matsalolin da mai gidan ta ya gada, ya kuduri aniyar shawo kan matsalolin da kasar ke fuskanta.

Kazalika ta ce Tinubu zai yi kokari wajen ganin ya gyara dukkan kurakuran da ya tarar a cikin kasar.

Sannan ta ce nan ba da jimawa ba ‘yan Kasar za su dawo cikin walwala da jindadi daga cikin halin matsin da suka tsinci kansu.

Continue Reading

Labaran jiha

Gwamnatin Kano Za Ta Buɗe Cibiyoyin Koyon Sana’o’in Dogaro Da Kai

Published

on

Gwamantin jihar Kano ta ce za ta buɗe cibiyoyin koyon aikin sana’o’in dogaro da kai a jihar.

Sannan gwamnatin jihar Kano ta rage kashi 50 cikin ɗari na rijistar shiga manyan makarantu a jihar.

Ragin ya shafi iya ɗalibai ƴan asalin jihar Kano ne kaɗai.

A wata sanarwa da kwamishinan ilimi mai zurfi a jihar Dakta Yusuf Ibrahim Ƙofar Mata ya sanyawa hannu, sanarwar ta ce an yanke hukuncin ne yayin wata ganawa da da gwamnan ya yi da shugabannin manyan makarantu a jihar.

Sanarwar ta ce an yi haka ne domin baiwa ɗalibai a jihar damar samun ilimi.

Haka kuma gwamnatin za ta buɗe cibiyoyin koyon sana’o’in dogaro da kai a jihar yadda matasa za su tsaya da ƙafarsu.

Gwamnatin ta ce ta na mayar da hankali domin bayar da ingantaccen ilimi domin cigaban jihar.

Dukkanin ɗalibai da ke karatu a kwalejiji da jami’o’i mallakin jihar Kano kuma su ka kasance yan asalin jihar za su amfana da ragin kudin.

Bai wa ɓangaren ilimi muhimmanci na dga manufofin Injiniya Abba Kabir Yusuf wanda ya sha alwashin haka tun lokacin yakin neman zaben sa.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: