Rahoto
Me yasa al’ummar Kano basu aminta da KAROTA ba? -Aliyu Sufyan


SHIN AKWAI AMFANIN HUKUMAR KAROTA A KANO?

Kowacce Jiha a kasar nan na da tsarin gudanarwarta ta fannoni da dama, ta bangaren zamantakewa da zuwa da tsari da Jihar zatayi tunkaho na gwada kwanji.
Nasan zakuyi mamakin mabudin rubutuna akan AMFANI KO RASHIN ALFANUN HUKUMAR KAROTA A Jihar Kano, Hukuma ce wadda tsohon Gwamnan Kano Dr Rabi’u Musa Kwankwaso ya kirkirota ta hanyar kwaikwaiyo makamanciyar hukumar da ke kula da tituna ta Jihar Ikko wato LAROTA.

Ayyukan wannan hukuma musamman anan kano shine; kula da tituna, magance haddura,da kuma motocin da suke lodi ba bisa ka’ida ba, da ma kula da motocin da suke shigowa daga wasu Jihohin don tabbatar da zaman lafiyar Jihar Kano da gudanar da rage cunkoson ababan hawa a Jihar da ta fi kowacce yawan al’umma da kuma ababan hawa.

A jihar Kano hukumar KAROTA a kiyasi tana da ma’aikata kimanin mutum 2,400 wadanda matasane da shekarunsu basu wuce daga 23 zuwa 40 ba, kuma dukkaninsu ‘yan asalin Jiha ne wadanda aka rage yawan matasa da basu da aikin yi.

A kwanakin baya Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bada damar sake daukar matasa masu matukar yawa a hukumar, sannan bayan nada Hon Baffa Baffa DanAgundi hukumar ta canja salon gudanarwarta ta gudanar da Basani-Ba Sabo domin bin ka’idar hanyoyi musamman don gudun hadura da ka iya zama ruwan dare a kano.
Hukumar a kwanakin baya ta samu nasarar gano wata mota cike da kwayoyi na bogi, wanda aka shigo da ita daga wata jiha a kasar nan, kiyasi ya nuna kusan magungunan na bogi sun kai Naira Miliyan 50 ko sama da haka, wanda dubban ‘yan asalin Kano idan sukayi amfani da wannan magani zasu iya kamuwa da cutar da ko dai ta zama ajalinsu, ko kuma kamuwa da cutar da warkewarta sai an sha wahala.
Matukar wannan hukuma na gudanar da irin wannan hukuma na gudanar da irin wannan aiki, me zai saka Kanawa suna kallonsu a matsayin BARAZANA ga masu amfani da ababan hawa? Mai Zai saka Kanawa bazasu kalli kokarin da Kannenmu, yayyenmu, sukeyi don guduwa tare mu tsira tare.
A kwanakin baya guda cikin matasa a KAROTA ya rasa ransa akan titin zuwa Airport, kuma a kokarinsa don ganin ya bi ka’idar aikinsa, sannan wani matashin shima Dan KAROTA a kwanaki biyu ya rasa ransa a kan Shatale-Talen NNPC dake Hotoro biyo bayan takeshi da wani dan Tirela yayi, shin wannan ba abun tambaya akai? Me yake Faruwa kannenmu suke rasa ransu a wannan aiki?
Na tattauna sosai da mutane daban-daban, inda kusan abin na faruwa ne ga rashin bin ka’idojin hanya da masu motoci, babura, da sauran ababan hawa ke yi a nan Kano, wanda kuma suna daukar ‘yan Karota a matsayin makiya wanda suke zaluntarsu, na tabbata idan kabi ka’idar hanya babu wani dan karota da zai nufeka da wata magana ta cewar ka taka doka.
Ya kamata KANAWA mu waye, mu sani cewar zaman lafiyar mu shine mu yi biyayya ga dukkanin dokar da aka gindaya mana, domin mu zama abin kwatance.
Na tabbata a misali a janye ‘yan KAROTA a Kano na wuni guda, Wallahi sai duk mai hawa abin hawa ya gane kurensa sakamakon irin gudunmawa da suke bayarwa akan manyan tituna, zaka tausaya musu idan hanyar Dan-Agundi, Bata, Bairut Road, ko kuma hanyar zuwa Kurna ta yadda suke kokari, komai ruwa, komai rana, komai wahala, amma bama gode musu sai dai mu nemi rayuwarsu, to ya kamata Gwamnati ta dau mataki mai karfi ga wanda yake cin zarafin yan karota musamman idan sun yi kokarin kawo gyara a aikinsu.
‘Yan Adaidaita sahu, masu hayis, da masu motocin amfani yau da kullum, mu baiwa ‘Yan karota hadin kai, wallahi ba karamin taimakawa al’umma suke yi ba, mu tsaya muyi tunani, kada son zuciya mu dinga kallonsu a matsayin makiya.
Kira ga shugaban hukumar KAROTA Hon Baffa Babba Dan-Agundi wannan kalubale ne akanka na kokarin fijiro da dabaru, hanyoyi, da salon da yaranka zasu sani wajen tunkarar wanda ya aikata laifi, sannan a dinga shirya musu Bita wanda kwararru zasu dinga jagoranta don kannenmu su sami kwarewa mai girma wajen ayyukansu.
Masha Allah, Allah ka zaunar da Kanon mu lafiya, ka baiwa shugabanninmu damar gudanar da adalci a tsakaninmu.
Aliyu Sufyan Alhassan
Head of Political Unit
Aminci Radio 103.9FM
Rahoto
Akwai Yiwuwar Kasuwanci Ya Tsaya Cak A Najeriya


Yayin da ya rage saura kwanaki goma kacal a dakatar da karɓar kuɗaɗe da aka sauyawa fasali a Najeriya, kasuwanci na fuskantar barazana cikin waɗannan kwaanaki.

Gwamnatin tarayya ta sauya fasalin naira 200, 500 da kuma naira 1,000 tare da sanya wa’adin ƙarshen watan Janairun da mu ke ciki a matsayin ranar karshe da za a daina karɓar tsofaffin kuɗi.
A sakamakon hakan ya sanya wasu da dama daga cikin ƴan kasuwa musamman a Kano cibiyar Kasuwanci, su ka tsayar da ranar Laraba a matsayin ranar da za su rufe amsar tsofaffin kuɗin da aka sauya.

A ɓangaren ƙananan ƴan kasuwa kuwa sun sanya ranar Talata domin daina karɓar kuɗaɗen tare da ƙoƙarin shigar da waɗanda ke hannunsu zuwa gaba.

Wajen da gizo ke saƙar shi ne, har a yanzu babu wadatattun sabbin nairar a hannun mutane.

A wani bincike da Matashiya TV ta yi, ta gano wasu yankuna da ake sanya wani kaso kafin shigar da kuɗi ga masu sana ar POS.
Wata majiya taa tabbatar da cewar,ana karɓar naira 3,000 a matsayin caji idan mutum ya na so a tura masa naira 100,000.
Ko za a iya samun wadataccen kuɗin zuwa watan Fabrairu?
Tambayar da wasu mutaane ƴan Najeriya ke yi bayan ƙorafin rashin wadatar sabbin kuɗi a hannunsu.
Sai dai bankin Najeriya CBN ya ce ya kafa wani tsari da zai dinga karɓar tsofaffin kuɗin a mataki na ƙananan hukumomi na Najeriya.
Ko sabon tsarin na CBN ya fara aiki?
Har yanzu mutane na kokawa a dangane da batun sauyin kuɗin yayin da bankune ke cike don shigar da waɗand ake hannunsu zuwa asusun ajiya.
Ta yaya kasuwanci zai tsayaa cak a Najeriya?
Duba ga rashin wadatar sabbin kuɗin a hannun jama’a tare da ƙoƙarin mayar da tsofaffin zuwa bankuna, hada-hadar kasuwar na iya samun naƙasu duba ga yanayin da aka saba yin kasuwanci.
Da yawan ƴan kasuwa na amfani da takardar kuɗi wajen saye ko sayarwa a kasuwannin Najeriya.
Haka kuma mutane da ke siyayya na har yanzu akwai ƙaraancin kuɗaɗe a hannunsu yayin da ya rage saura kwanaki goma a dakatar da karɓar kuɗin a hukumance.
Ko za a iya samun sasdauci?
Akwai yuwuwar hakan duba ga cewa gwamnati ba ta yi aalbashi ba kuma ana kyautaa zaton biyan albashin da za a yi za a yi amfani da saabbin kuɗi qajen biya.
Rahoto
Dala Bilayan 12 ake asara a Najeriya Sakamakon Rikicin Makiyaya da Manoma


An samu rahoton asarar akalla dala biliyan 12 a Nijeriya, sakamakon rikicin manoma da makiyaya da ya mamaye sassa daban daban na kasar.

Daraktan kungiyar sa kai ta Mercy Corps, Ndubisi Anyanwu,ne ya sanar da hakan a ranar Talata a zantawarsa da manema labarai jim kadan bayan ganawa da jami’an gwamnati a garin Makurdi.
“a cewarsa sun yi kiyasin asarar akalla $12b a kowacce shekara sakamakon rikicin makiyaya da manoma. “Wannan wani babban al’amari ne kuma da zai iya shafar kasar baki daya,”

Anyanwu ya kara da cewa akwai bukatar a mayar da hankali kan rikici tsakanin makiyaya da manoma, yana mai cewa wannan ne ma dalilin da yasa kungiyar ta shiga cikin lamarin.

Ya yi nuni da cewa kungiyar Mercy Corps, da aka samar da ita karkashin hukumar USAID, ta mayar da hankali kan gina zaman lafiya na watanni 60 a Benue da wasu jihohin jihar.

Tun farko, shugabannin kananan hukumomi a jawabansu daban daban sun lissafa rashin aikin yi, rashin ababen more rayuwa daga cikin dalilan haddasa rikicin makiyaya da manoma.
Rahoto
An samu asarar rayuka 415 a Najeriya daga watan Yuli zuwa yanzu


Wasu Alkaluman bincike na nuni da cewar akalla mutane 415 aka kashe a Najeriya a watan Yulin da ya gabata sakamakon hare hare da kuma tashin hankalin da ake cigaba da samu a cikin kasar.

Rfi hausa ta rawaito cewa Wata kungiya da ta kira kan ta ‘Nigeria Mourn’ tace an fi samun kashe kashen dake da nasaba da hare haren Yan bindiga da rikicin yan tada kayar baya da kuma barayin shanu ne a Jihohin Kaduna da Borno da Katsina.
Alkaluman kungiyar sun ce daga cikin Jihohi 21 da aka kashe mutane 415, Jihar Kaduna ke sahun gaba da mutane 139, sai Barno mai 113, Katsina na da 80, Kogi 17, Nasarawa 13, Taraba 10, Benue 9 sai kuma Ebonyi mai 8.

Sauran sun hada da Zamfara mai mutane 7, Plateau 5, Edo da Akwa Ibom da Lagos na da bibiyu, sai kuma Jihohin Oyo da Imo da Rivers da Cross Rivers da Ogun da Bayelsa da Delta da kuma Kebbi dake da guda-guda.


-
Mu shaƙata10 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Labarai8 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?