Labaran jiha
Shin Karota na da hurumi wajen kama kayan maye?


Idan ba a manta ba a kwananan ne Hukumar da ke lura da zirga zirgar ababen hawa ta jihar Kano KAROTA ta kame wani kayan maye samfurin Sholisho katan Dari da hamsin da bakwai a wani gida da ke kan titin Emir a unguwar Sabon gari da ke Kano.

Wanda kudin sa ya Kai Miliyan ashirin.
Idan ba a manta ba a kwanan baya ma hukumar ta kama wasu kwayoyin magani da ake zargin marasa kyau ne.

Mujallar Matashiya ta nemi jin ta bakin Hukumar Karota kan tana da alhakin kame kayan shaye- Shaye.

Wannan kamen kayan maye da hukumar Karota tayi na daya daga cikin ayyukanta na Binciken ababen hawa tare da gano irin nau’in kayan da aka shigo dasu jihar Kano.

Kamar yadda jami’in hulda da jama’a na hukumar KAROTA Nablisi Abubakar Ahmad ya ce hukumar karota na cikin jami’an hadin gwiwa dake yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a jihar Kano.
Nablisi yayi Kira ga Al’umma da su rika sa idanu akan irin kayan da ake shigo dasu tare da Kai rahoto ga jami’an tsaro.
Labaran jiha
Hukumar Hisba A Kano Ta Kori Daya Daga Cikin Kwamandojin Ta


Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kori daya daga cikin kwamandojin ta, tare da binciken wasu mutane biyar bisa laifin kawo cikas a yaki da lalata da zamantakewa a jihar.

Shugaban hukumar Sheik Aminu Ibrahim Daurawa ya ce an samu kwamandan da aka kora da aikata rashin da’a, yayin da ake ci gaba da binciken sauran wasu mutane biyar.
Ya bayyana cewa jami’in da aka kora ya saba hada kai da mugayen mutane don tafka munanan ayyuka a jihar.

Ya ce, sun kori Mataimakin Sufeto na Hisbah (DSH) tare da bayyana cewa ana neman sa, duk inda aka same shi a kama shi a gurfanar da shi a gaban kuliya.

A cewar sa ya kan hada kai da masu gudanar da otal din don kada hukumar Hisbah ta mamaye otal din nasu a yayin gudanar da ayyukanta.

Daurawa ya kuma musanta zargin cewa jami’anta sun aske gashin wani da ba dan asalin jihar ba da kwalba bayan sun kai farmaki gidan mata masu zaman kansu a jihar.
Wani mai amfani da kafar sadarwa ta Facebook ne ya yi wannan zargin, amma Daurawa ya yi watsi da batun wanda ya alakanta a matsayin masu tada zaune tsaye.
Labaran jiha
Gwamnatin Tinubu Ta Maida Hankali Ne Kan Abubuwan Da Suka Addabi Kasar-Remi Tinubu


Mai dakin shugaban kasa Bola Tinubu Remi Tinubu ta bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta mayar da hankali ne akan gyaran matsalolin da suka addabi Kasar.

Remi ta bayyana haka ne a yayin da ta halarci coci domin yin addu’o’i da kuma bikin cikar Kasar shekaru 63 da samun ‘yancin kai a ranar Lahadi.
Uwar gidan shugaban ta ce mai gidan ta ya tarar da tarin matsaloli masu yawa daga gwamnatin da ya gada.

Remi ta kara da cewa duk da tarin matsalolin da mai gidan ta ya gada, ya kuduri aniyar shawo kan matsalolin da kasar ke fuskanta.

Kazalika ta ce Tinubu zai yi kokari wajen ganin ya gyara dukkan kurakuran da ya tarar a cikin kasar.

Sannan ta ce nan ba da jimawa ba ‘yan Kasar za su dawo cikin walwala da jindadi daga cikin halin matsin da suka tsinci kansu.
Labaran jiha
Gwamnatin Kano Za Ta Buɗe Cibiyoyin Koyon Sana’o’in Dogaro Da Kai


Gwamantin jihar Kano ta ce za ta buɗe cibiyoyin koyon aikin sana’o’in dogaro da kai a jihar.

Sannan gwamnatin jihar Kano ta rage kashi 50 cikin ɗari na rijistar shiga manyan makarantu a jihar.
Ragin ya shafi iya ɗalibai ƴan asalin jihar Kano ne kaɗai.

A wata sanarwa da kwamishinan ilimi mai zurfi a jihar Dakta Yusuf Ibrahim Ƙofar Mata ya sanyawa hannu, sanarwar ta ce an yanke hukuncin ne yayin wata ganawa da da gwamnan ya yi da shugabannin manyan makarantu a jihar.

Sanarwar ta ce an yi haka ne domin baiwa ɗalibai a jihar damar samun ilimi.

Haka kuma gwamnatin za ta buɗe cibiyoyin koyon sana’o’in dogaro da kai a jihar yadda matasa za su tsaya da ƙafarsu.
Gwamnatin ta ce ta na mayar da hankali domin bayar da ingantaccen ilimi domin cigaban jihar.
Dukkanin ɗalibai da ke karatu a kwalejiji da jami’o’i mallakin jihar Kano kuma su ka kasance yan asalin jihar za su amfana da ragin kudin.
Bai wa ɓangaren ilimi muhimmanci na dga manufofin Injiniya Abba Kabir Yusuf wanda ya sha alwashin haka tun lokacin yakin neman zaben sa.
-
Mu shaƙata10 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Labarai8 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?