Connect with us

Labarai

Yadda aka gudanar da zaɓen cike gurbi a Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta saka yau 25 ga watan janairun shekarar 2020 a matsayin ranar da za a gusanar da zaɓen cike gurbin wasu daga cikin ƴan majalisar wakilai ta tarayya da wasu ƴan majalisar dokoki ta jiha.

Mujallar Matashiya ta zagaya wasu daga cikin mazaɓun ƙananan hukumomin Doguwa, Tudun Wada, da Bebeji.

A ƙaramar hukumar Tudun wada mun zagawa mazaɓu da dama inda muka riski jama a na gudanar da zaɓe a wasu wuraren yayinda wasu mazaɓun tuni aka kammala zaɓe a wajen.

Yayin zantawarmu da guda cikin masu yiwa ƙasa hidima da ya buƙaci a sakaye sunansa, ya bayyana mana cewar masu kaɗa ƙuri a ba su fito sosai ba kamar yadda ya ce kashi ɗaya bisa uku ne suka fito a mazaɓar da yayi aikin zaɓen.

A ƙaramar hukumar Doguwa mun zagaya mazaɓu da dama ciki har da mazaɓun da ke cikin garin Daɗin Kowa, Riruwai da sauransu inda a nan ma muka iske mutane na gudanar da harkokinsu da misalin ƙarfe 3 na rana, bayan da muka tuntuɓi wasu daga cikin mazauna garin sun bayyana cewar tun tuni aka kammala zaɓen yayin da kowa ya koma kasuwa don gudanar da harkokinsu, sai dai a mazaɓun ma ba a samu fitowar mutane da yawa ba.

A ƙaramar hukumar bebeji ma haka lamarin yake na rashin fitowar mutane.

A zaɓen da ya gudana a yau an samu wadataccen tsaro kuma babu wani waje da aka samu hargitsi yayin gudanar da zaɓen har aka kammalashi.

Ƙananan hukumomin Doguwa da Tudun wada dai na da wakili ɗaya a zauren majalisa kamar yadda ƙaramar Hukumar Ƙiru da Bebeji ma ke da wakili a zauren.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Iyayen Ɗaliban Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Jami’ar Tarayya Da ke Gusau Sun Gudanar Da Zanga-Zanga

Published

on

Iyayen dalibai matan da aka yi garkuwa da su a jami’ar tarayya da ke garin Gusau da ke Jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a gidan gwamnatin Jihar.

Iyayen sun yi zanga-zangar ne domin neman a gaggauta sako musu ‘ya’yansu da masu garkuwa suka yi garkuwa dasu a cikin Jami’ar.

Masu zanga-zangar sun kuma nemi da gwamnan Jihar Dauda Lawal Dare da sauran hukumomin tsaron Jihar da su yi duk mai yuwuwa wajen ganin an kubtar da ‘ya’yannasu cikin koshin lafiya.

Kazalika sun ce ‘yan bindigar sun neme wasu daga cikin iyayen daliban kan cewa ba za su sako daliban ba harsai sun tattàuna da gwamnatin Jihar.

Inda suka nemi da gwamnatin ta yi duk mai yuwuwa wajen ganin an ceto ragowar wadanda ke hannun batagarin.

Masu garkuwar, sun yi garkuwa da daliban ne tun a ranar 22 ga watan Shekarar da mu ke ciki inda suka yi garkuwa da dalibai Mata 24 da wasu ma’aikata 10 a cikin Jami’ar, a lokacin da suka kai hari garin sabon Gida garin da dakunan kwana daliban suke.

Amma bayan garkuwa da daliban jami’an tsaro sun kubtar da dalibai 13 daga cikinsu Leburori Biyu, yayin da ragowar ke hannun maharan.

 

 

Continue Reading

Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Bayar Da Umarnin Yin Bincike Kan Harin Bom Ɗin Da Ya Kashe Masu Taron Maulidi A Kaduna

Published

on

Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani ya bayar da umarnin gudanar da bincike akan hallaka mutane da dama da jirgin yakin sojin Najeriya ya yi a Jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da ya fitar, tare da mika sakon jaje ga al’ummar Jihar.

Uba Sani ya ce gwamnatinsa ta kuduri aniyar daukar matakin kaucewa kara faruwar hakan.

Gwamnan ya kuma bai’wa al’ummar Jihar tabbacin cewa za a tabbatar da tsaro, da bai’wa mutanen Jihar Kariya a lokacin da ake kokarin kawar da ‘yan ta’adda da sauran batagari a Jihar.

Gwamna Uba Sani ya bayar da umarnin kwashe wadanda suka jikkata zuwa asibitin koyarwa na Barau Dikko, domin ba su kulawar gaggawa da kuma daukar nauyinsu.

Jirgin ya hallaka mutanen a ranar Lahadi, a lokacin da suke tsaka da gudanar da bikin Mauludin a karamar Igabi ta Jihar bayan sanya musu bom da jirgin yayi har sau biyu.

 

 

Continue Reading

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Umarci A Yi Bincike Kan Harin Sojojin Da Ya Kashe Mutane A Kaduna

Published

on

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar da umarnin gudanar da bincike akan mutanen da jirgin yakin sojin sama ya hallaka a Jihar Kaduna a lokacin da suke gudanar da taron mauludi a yankin Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi ta Jihar.

Shugaban ya bayar da umarnin ne a safiyar yau Talata, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawunsa Ajuri Ngelale ya fitar.

Tinubu ya nuna alhininsa akan lamarin tare da mika sakon ta’aziyyarsa ga gwamnatin Jihar da ‘yan uwa da iyalan wadanda suka rasa rayukansu.

Sanarwar ta ce shugaban ya bayar da umarnin a gudanar da bincike da kuma bai’wa wadanda suka jikkata kulawa ta musamman.

Tinubu ya kuma bukaci da mutane su bai’wa jami’an tsaron hadin kai wajen gudanar da bincike.

Sannan Tinubu yayi addu’ar neman gafara da rahmar Allah ga wadanda suka rasa rayukansu.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: