Labarai
Cancanta ce ta sa muka karrama Rarara – Ƙungiyar ɗaliban Arewa


Daga Isah Bawa Doro

Wata kungiyar daliban arewacin Nijeriya mai suna ‘Association of Northern Nigerian Students’ (ANNS) suka karrama fitaccen mawakin siyasar nan wato Dauda Kahutu Rarara.
ANNS kungiyar dalibai ce wadda ta kunshi jihohin Arewa goma 19 da kuma babban birnin tarayya Abuja. Daliban sun ba Rarara lambar girmamawar ne a harabar Otal din Tumfure da ke garin Gombe.

Da ya ke yi Kannywood Exclusive karin bayani game da karramawar, shugaban gudanarwa na kungiyar na shiyyar arewa maso gabas, Kwamred Sadiƙ Sabo ya ce: “Ita daman kungiyar mu ta kan yi duba a cikin al’umma ta zakulo wani mutum, wanda ya kware wajen yi wa al’umma hidima a kasa baki daya.

Wannan kungiyar ta zakulo Rarara, kuma an zauna an ga cancantar sa, kafin a karrama shi. Shi ya kasance tsaka tsakiya tsakanin talakawa da gwamnatin kasar nan. Wanda ko a rediyo ba lallai ne ka san yanayin da kasa ta ke ci ba.

Amma cikin baiwar da Allah ya ba shi, ya kan dauki korafe-korafe na talakawa sannan ya isar da sakon su ta sigar waka, kuma sakon sa yana isa a wurin ‘yan siyasa, wanda idan su ka ji matsalolin sai su duba, su ga ta inda za su fara gyara.
A gefe guda kuma shi wannna mawakin gwani ne da ya shahara wurin hidimar al’umma, a ko’ina za ka gan shi, ba za ka gan shi shi kadai ba sai da dandazon al’umma. Maganar gaskiya idan mutum ba mai alheri ba ne, ba lallai ba ne ka ga jama’a na dabaibaye shi ba. Wannan yana daga cikin dalilin da yasa wannan kungiya ta mu ta karrama shi domin kara masa kwarin gwiwa bisa ayyukan da ya ke yi na ci-gaban al’umma da kuma talakawa” a cewar shugaban ƙungiyar kwamared sadiƙ.
Labarai
Iyayen Ɗaliban Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Jami’ar Tarayya Da ke Gusau Sun Gudanar Da Zanga-Zanga


Iyayen dalibai matan da aka yi garkuwa da su a jami’ar tarayya da ke garin Gusau da ke Jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a gidan gwamnatin Jihar.

Iyayen sun yi zanga-zangar ne domin neman a gaggauta sako musu ‘ya’yansu da masu garkuwa suka yi garkuwa dasu a cikin Jami’ar.
Masu zanga-zangar sun kuma nemi da gwamnan Jihar Dauda Lawal Dare da sauran hukumomin tsaron Jihar da su yi duk mai yuwuwa wajen ganin an kubtar da ‘ya’yannasu cikin koshin lafiya.

Kazalika sun ce ‘yan bindigar sun neme wasu daga cikin iyayen daliban kan cewa ba za su sako daliban ba harsai sun tattàuna da gwamnatin Jihar.

Inda suka nemi da gwamnatin ta yi duk mai yuwuwa wajen ganin an ceto ragowar wadanda ke hannun batagarin.

Masu garkuwar, sun yi garkuwa da daliban ne tun a ranar 22 ga watan Shekarar da mu ke ciki inda suka yi garkuwa da dalibai Mata 24 da wasu ma’aikata 10 a cikin Jami’ar, a lokacin da suka kai hari garin sabon Gida garin da dakunan kwana daliban suke.
Amma bayan garkuwa da daliban jami’an tsaro sun kubtar da dalibai 13 daga cikinsu Leburori Biyu, yayin da ragowar ke hannun maharan.
Labarai
Gwamna Uba Sani Ya Bayar Da Umarnin Yin Bincike Kan Harin Bom Ɗin Da Ya Kashe Masu Taron Maulidi A Kaduna


Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani ya bayar da umarnin gudanar da bincike akan hallaka mutane da dama da jirgin yakin sojin Najeriya ya yi a Jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da ya fitar, tare da mika sakon jaje ga al’ummar Jihar.
Uba Sani ya ce gwamnatinsa ta kuduri aniyar daukar matakin kaucewa kara faruwar hakan.

Gwamnan ya kuma bai’wa al’ummar Jihar tabbacin cewa za a tabbatar da tsaro, da bai’wa mutanen Jihar Kariya a lokacin da ake kokarin kawar da ‘yan ta’adda da sauran batagari a Jihar.

Gwamna Uba Sani ya bayar da umarnin kwashe wadanda suka jikkata zuwa asibitin koyarwa na Barau Dikko, domin ba su kulawar gaggawa da kuma daukar nauyinsu.

Jirgin ya hallaka mutanen a ranar Lahadi, a lokacin da suke tsaka da gudanar da bikin Mauludin a karamar Igabi ta Jihar bayan sanya musu bom da jirgin yayi har sau biyu.
Labarai
Shugaba Tinubu Ya Umarci A Yi Bincike Kan Harin Sojojin Da Ya Kashe Mutane A Kaduna


Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar da umarnin gudanar da bincike akan mutanen da jirgin yakin sojin sama ya hallaka a Jihar Kaduna a lokacin da suke gudanar da taron mauludi a yankin Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi ta Jihar.

Shugaban ya bayar da umarnin ne a safiyar yau Talata, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawunsa Ajuri Ngelale ya fitar.
Tinubu ya nuna alhininsa akan lamarin tare da mika sakon ta’aziyyarsa ga gwamnatin Jihar da ‘yan uwa da iyalan wadanda suka rasa rayukansu.

Sanarwar ta ce shugaban ya bayar da umarnin a gudanar da bincike da kuma bai’wa wadanda suka jikkata kulawa ta musamman.

Tinubu ya kuma bukaci da mutane su bai’wa jami’an tsaron hadin kai wajen gudanar da bincike.

Sannan Tinubu yayi addu’ar neman gafara da rahmar Allah ga wadanda suka rasa rayukansu.
-
Mu shaƙata10 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Labarai8 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?