Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya zata Raba Hatsi Tan Dubu saba’in ga Mabukata

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da fitar da tan Dubu saba’in daga ma’adanar hatsi ta kasa don raba wa mabukata a kasar nan a matsayin hanyar saukaka barnar da cutar coronavirus ta yi.

Sakataren gwamnatin tarayya kuma shugaban kwamitin shugaban kasa a kan yaki da cutar COVID-19, Boss Mustapha, ne ya sanar da hakan a Abuja yayin jawabi karo na uku na PTF a ranar Laraba.

Kamar yadda yace, tan Dubu sittin sau dubu na hatsi za a raba wa jama’ar jihohi birnin tarayya Abuja, Legas da jihar Ogun.
Sauran tan goma sau dubu din kuwa za a raba ne ga mabukatan da ke sauran jihohin Najeriya.

Boss Mustapha Ya kara da cewa PTF ta habbaka dokoki da sabbin tsare-tsare yayin rufe jihohin nan, wadanda za su zagaye kasar nan ta hannun cibiyoyin tsaro.

Idan zamu tuna, a ranar Lahadi ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarnin rufe jihohin Lagos da Ogun tare da babban birnin tarayya.
Hakan ta faru ne kuwa don hana yaduwar cutar coronavirus a kasar Najeriya.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Gobara Ta Kama A Kotun Ƙoli Ta Najeriya A Abuja

Published

on

Rahotanni daga baban birnin tarayyar Najeriya Abuja na tabbatar da cewar kotun ƙoli ta kama da wuta.

Ofishin alƙalai uku aka ruwaito sun ƙone bayan tashin gobarar.

Godan jaridar Arise ya ruwaito cewar, wutar ta kama wai ɓangare na cikin kotun.

Sai dai ba a san sanadin tashin gobarar ba.

Wannan dai itace gobara da aka yi a kusa-kusa wadda ta shafi ofishin gwamnati.

Ko a watan Mayun shekarar da mu ke ciki, gobara ta kama a rundunar sojin samar Najeriya.

Yayin da a shekarar da ta gabata ta 2023 ma’aikatar kuɗi ta tarayya wani ɓangare ya kama da wuta.

Continue Reading

Labarai

Amuruka Ta Gargaɗi Ƴan Ƙasar Mazauna Najeriya Kan Ziyartar Wasu Jihohi Har Da Kano

Published

on

Ƙasar Amurka ta gargaɗi ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su kiyaye wajen ziyartar wasu jihohi da ka iya faɗawa cikin hatsari.

Sanarwar na zuwa ne bayan gudanar da wani bincike da su ka gano an samu ƙaruwar aikata manyan laifuka a jihohin.

Jihohin sun haɗa da Borno, Adamawa, Yobe, Kogi, Bauchi, Kaduna, Kano, Gombe, Bayelsa, Rivers, Enugu da jihar Bayelsa.

Sauran jihohin su ne Imo, SokOto, Zamfara, Katsina, da jihar Abia.

Ƙasar ta gargaɗi mutanenta da su kiyaye wajen ziyartar waɗannan jihohi domin su na iya faɗawa cikin tarkon masu garkuwa da mutane ko wasu miyagun laifuka.

Binciken da su ka yi sun gano cewar masu satar mutane domin neman kuɗin fansa na amfani da ƙarin mutane a wasu sassa domin cimma muradinsu.

Sannan gwamnatin Amurukan ta buƙaci ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su ƙara sanya idanu a kan dukkanin zirga-zirgarsu don gudun faɗawa hatsari.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Rundunar Tsaro A Taraba Sun Kama Mutane 20 Sanye Da Kayan Sojoji

Published

on

Rundunar ƴan sanda a jihar Taraba ta ce ta kama wasu mutane 20 da take zargi da yin garkuwa da mutane.

Nasarar na zuwa ne bayan tattara bayanan sirri da aka yi bayan karɓar ƙorafin jama’a dangane da garkuwa da mutane da ake yawan samu a ɓangare daban-daban na jihar.

Mai magana da yawun yan sandan jihar Abdullahi Usman ya ce waɗanda aka kama sun amsa laifinsu.

Ya ce sun kama bindigu ƙirar AK47 guda uku da kuma wata bindiga daban.

Sannan ya ce mutanen da ake zargi sun karɓi kuɗi sama da naira miliyan 30 daga ƴan uwan waɗanda su ka yi garkuwa da su.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar ya ce rundunar ba za ta gaza ba wajen farautar mutanen da ke aikata laifuka a jihar.

Sannan za su ci gaba da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: