Ma’aikatar kula da aikin Hajji da Umrah ta kasar saudiyya ta yi kira ga kasashen duniya da su dakatar da karbar kudaden aikin hajjin bana daga hannun jama’a.
A sakon da ministan ma’aikatar aikin hajji da Umrah ya wallafa a shafinsa na Tiwita,
ministan ya ce mahukunta sun yanke wannan hukunci ne a dalilin barkewar cutar coronaviorus da ya karade duniya.
Ya kuma de dole sai an dan dakata tukunna zuwa aga abin da hali zai yi.
Bayan haka kuma ma’aikatar ta ce Saudiyya ta mayar wa da duk wanda da ya biya kudin bizar Umran na bana zuwa kasar.
Sannan kuma duk mutanen da suka makale a Makka sakamakon dokar garkame kasashensu za su ci gaba zama a kasar kuma za a basu kyakkyawar kulawa har zuwa lokacin da kasashen su za su bude filayen jiragen su amaido da su gida.
Kasar Saudiyya na daga cikin kasashen da suke fama da cutar coronavirus.
Duk da dai suna ta kokarin ganin cutar bai karade kasar ba.
An rufe masallatan kasar banda masallacin harami da na madina domin gudun kada cutar ya kai ga wadannan garuruwa.