Rahoto
Duk Kasahen da suka Dogaro da Manfetur, suna cikin Tsaka Mai Wuya


Tun bayan Bullar Cutar corona virus ta raunana tattalin arzikin kasahen duniya ciki har da Najeriya.
Wannan dalili yasa farashin ‘danyen man fetur ke ta sauka kasa irin yadda bai taba kasancewa ba a tarihi .

A yanzu kowace gangar ‘danyen mai ana siyar dashi akan dalar amurka 11 ($11) wanda a hakan ma Najeriya bata iya siyar da man duk da wasu saukin da akai wa masu siya.
Kasashen da suka dogara da ‘danyen mai a matsayin babban hanyar shigar su a halin yanzu suna cikin tsaka mai wuya.
Najeriya ta na daya daga cikin kasashen da suke dagaro da man fetur sosai a matsayin kudin tafiyar da harkokin kasar.

Masana da masu ruwa da tsaki a harkar sun bayyana cewa yanzu akwai miliyoyin gangar mai a ajiye wanda ake jiran masu siya, Najeriya na fusakantar kalubalen karyewar farashin mai da kuma na masu siyan albarkatun man a kasuwannin duniya. Gashi kasar bata yi wani shiri na musamman ba domin adana ‘danyen albarkatun man ba .

Muryar yanci ta Rawaito cewa Wannnan kalubalen na karyewar darajar mai a kasuwannin duniya ba karamar barazana bace ga kasashe masu tasowa da kuma kasashen da mai ne babban hanyar samun kudaden shigar su .

Rahoto
Akwai Yiwuwar Kasuwanci Ya Tsaya Cak A Najeriya


Yayin da ya rage saura kwanaki goma kacal a dakatar da karɓar kuɗaɗe da aka sauyawa fasali a Najeriya, kasuwanci na fuskantar barazana cikin waɗannan kwaanaki.

Gwamnatin tarayya ta sauya fasalin naira 200, 500 da kuma naira 1,000 tare da sanya wa’adin ƙarshen watan Janairun da mu ke ciki a matsayin ranar karshe da za a daina karɓar tsofaffin kuɗi.
A sakamakon hakan ya sanya wasu da dama daga cikin ƴan kasuwa musamman a Kano cibiyar Kasuwanci, su ka tsayar da ranar Laraba a matsayin ranar da za su rufe amsar tsofaffin kuɗin da aka sauya.

A ɓangaren ƙananan ƴan kasuwa kuwa sun sanya ranar Talata domin daina karɓar kuɗaɗen tare da ƙoƙarin shigar da waɗanda ke hannunsu zuwa gaba.

Wajen da gizo ke saƙar shi ne, har a yanzu babu wadatattun sabbin nairar a hannun mutane.

A wani bincike da Matashiya TV ta yi, ta gano wasu yankuna da ake sanya wani kaso kafin shigar da kuɗi ga masu sana ar POS.
Wata majiya taa tabbatar da cewar,ana karɓar naira 3,000 a matsayin caji idan mutum ya na so a tura masa naira 100,000.
Ko za a iya samun wadataccen kuɗin zuwa watan Fabrairu?
Tambayar da wasu mutaane ƴan Najeriya ke yi bayan ƙorafin rashin wadatar sabbin kuɗi a hannunsu.
Sai dai bankin Najeriya CBN ya ce ya kafa wani tsari da zai dinga karɓar tsofaffin kuɗin a mataki na ƙananan hukumomi na Najeriya.
Ko sabon tsarin na CBN ya fara aiki?
Har yanzu mutane na kokawa a dangane da batun sauyin kuɗin yayin da bankune ke cike don shigar da waɗand ake hannunsu zuwa asusun ajiya.
Ta yaya kasuwanci zai tsayaa cak a Najeriya?
Duba ga rashin wadatar sabbin kuɗin a hannun jama’a tare da ƙoƙarin mayar da tsofaffin zuwa bankuna, hada-hadar kasuwar na iya samun naƙasu duba ga yanayin da aka saba yin kasuwanci.
Da yawan ƴan kasuwa na amfani da takardar kuɗi wajen saye ko sayarwa a kasuwannin Najeriya.
Haka kuma mutane da ke siyayya na har yanzu akwai ƙaraancin kuɗaɗe a hannunsu yayin da ya rage saura kwanaki goma a dakatar da karɓar kuɗin a hukumance.
Ko za a iya samun sasdauci?
Akwai yuwuwar hakan duba ga cewa gwamnati ba ta yi aalbashi ba kuma ana kyautaa zaton biyan albashin da za a yi za a yi amfani da saabbin kuɗi qajen biya.
Rahoto
Dala Bilayan 12 ake asara a Najeriya Sakamakon Rikicin Makiyaya da Manoma


An samu rahoton asarar akalla dala biliyan 12 a Nijeriya, sakamakon rikicin manoma da makiyaya da ya mamaye sassa daban daban na kasar.

Daraktan kungiyar sa kai ta Mercy Corps, Ndubisi Anyanwu,ne ya sanar da hakan a ranar Talata a zantawarsa da manema labarai jim kadan bayan ganawa da jami’an gwamnati a garin Makurdi.
“a cewarsa sun yi kiyasin asarar akalla $12b a kowacce shekara sakamakon rikicin makiyaya da manoma. “Wannan wani babban al’amari ne kuma da zai iya shafar kasar baki daya,”

Anyanwu ya kara da cewa akwai bukatar a mayar da hankali kan rikici tsakanin makiyaya da manoma, yana mai cewa wannan ne ma dalilin da yasa kungiyar ta shiga cikin lamarin.

Ya yi nuni da cewa kungiyar Mercy Corps, da aka samar da ita karkashin hukumar USAID, ta mayar da hankali kan gina zaman lafiya na watanni 60 a Benue da wasu jihohin jihar.

Tun farko, shugabannin kananan hukumomi a jawabansu daban daban sun lissafa rashin aikin yi, rashin ababen more rayuwa daga cikin dalilan haddasa rikicin makiyaya da manoma.
Rahoto
An samu asarar rayuka 415 a Najeriya daga watan Yuli zuwa yanzu


Wasu Alkaluman bincike na nuni da cewar akalla mutane 415 aka kashe a Najeriya a watan Yulin da ya gabata sakamakon hare hare da kuma tashin hankalin da ake cigaba da samu a cikin kasar.

Rfi hausa ta rawaito cewa Wata kungiya da ta kira kan ta ‘Nigeria Mourn’ tace an fi samun kashe kashen dake da nasaba da hare haren Yan bindiga da rikicin yan tada kayar baya da kuma barayin shanu ne a Jihohin Kaduna da Borno da Katsina.
Alkaluman kungiyar sun ce daga cikin Jihohi 21 da aka kashe mutane 415, Jihar Kaduna ke sahun gaba da mutane 139, sai Barno mai 113, Katsina na da 80, Kogi 17, Nasarawa 13, Taraba 10, Benue 9 sai kuma Ebonyi mai 8.

Sauran sun hada da Zamfara mai mutane 7, Plateau 5, Edo da Akwa Ibom da Lagos na da bibiyu, sai kuma Jihohin Oyo da Imo da Rivers da Cross Rivers da Ogun da Bayelsa da Delta da kuma Kebbi dake da guda-guda.


-
Mu shaƙata10 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Labarai8 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?