Connect with us

Labaran jiha

Al’umma sai sun bada gudunma don kawo karshen Matsalar tsaro a jihar Katsina

Published

on

DAGA RABIU SANUSI KATSINA.

An Bukaci al’ummar da ke zaune a yankunan da matsalolin tsaro ya addaba, da su taimaka wa jami’an tsaro da bayanan sirri dan a samu damar dakile ma su tada kayar baya a wa su sassa na jihar katsina.

babban mai ba gwamnan jihar katsina shawara kan harkokin tsaro Alh, Ibrahim Ahmad, shine ya yayi wannan Kira a yayin wata Ganawa da wakilin mu na katsina ranar litinin.

Hon Ibrahim ya bayyana cewa a kokarin gwamnatin Rt Hon Aminu Bello Masari na kawo zaman lafiya a fadin jihar yasa mai girma gwamna ya bukaci taimako na musamman daga gwamnatin tarayya, kuma cikin yardar Allah an samu nasarar aiko da jami’an tsaro na musamman.

Haka zalika hon Ibrahim yayi Kira ga Al’umma da a tabbatar da cewa ana sanar da jami’an tsaro wani abu dake faruwa.

A cewarsa jami’an tsaro babu abin da su ke bukata face hadin kan mazauna yankunan da abin ya ke faruwa, inda ya bayyana wannan ne kadai hanyar da za su iya cimma ma su laifin cikin sauki.

Ibrahim Ahmad ya kuma jinjina ma mai girma shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa amsa kukan da al’ummar jihar katsina takai kan matsalar tsaro kuma ta amsa ta turo dauki.

Haka zalika ya nuna godiyar shi ga mai girma gwamna akan yunkurin shi na samar da zaman lafiya ga al’ummar jihar katsina, haka zalika ya yaba da irin kokarin jami’an tsaro da su ke fafatawa a wannan yunkuri na dakile Yan ta’adda a arewa maso gabas da yamma na kasar nan.

Daga karshe ya yi albishir ga manoman yankin da su kara addu’a dan idan Allah ya yarda za su cigaba da ayukan su na gona kamar yadda aka saba yi.

Click to comment

Leave a Reply

Labaran jiha

Gwamnatin Kano Za Ta Buɗe Cibiyoyin Koyon Sana’o’in Dogaro Da Kai

Published

on

Gwamantin jihar Kano ta ce za ta buɗe cibiyoyin koyon aikin sana’o’in dogaro da kai a jihar.

Sannan gwamnatin jihar Kano ta rage kashi 50 cikin ɗari na rijistar shiga manyan makarantu a jihar.

Ragin ya shafi iya ɗalibai ƴan asalin jihar Kano ne kaɗai.

A wata sanarwa da kwamishinan ilimi mai zurfi a jihar Dakta Yusuf Ibrahim Ƙofar Mata ya sanyawa hannu, sanarwar ta ce an yanke hukuncin ne yayin wata ganawa da da gwamnan ya yi da shugabannin manyan makarantu a jihar.

Sanarwar ta ce an yi haka ne domin baiwa ɗalibai a jihar damar samun ilimi.

Haka kuma gwamnatin za ta buɗe cibiyoyin koyon sana’o’in dogaro da kai a jihar yadda matasa za su tsaya da ƙafarsu.

Gwamnatin ta ce ta na mayar da hankali domin bayar da ingantaccen ilimi domin cigaban jihar.

Dukkanin ɗalibai da ke karatu a kwalejiji da jami’o’i mallakin jihar Kano kuma su ka kasance yan asalin jihar za su amfana da ragin kudin.

Bai wa ɓangaren ilimi muhimmanci na dga manufofin Injiniya Abba Kabir Yusuf wanda ya sha alwashin haka tun lokacin yakin neman zaben sa.

Continue Reading

Labaran jiha

Jami’an Sojin Najeriya Sun Lalata Maboyar ‘Yan Bindiga A Katsina Da Sokoto

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta samu nasarar lalata maɓoyar ƴan bindiga tare da wasu da dama a jihohin Katsina da Sokoto.

Jami’an sunƙato makamai da dama daga wajen yan bindiga.

Rundunar Operation Hadarin Daji sun samu narar ne a ranar 3 ga watan Agusta da mu ke ciki yayin da su ka kai hari ƙaramar hukumar Isa a jihar Sokoto.

Haka kuma runduna ta Takwas sun shiga Sabon Birni sannan su ka kusta dazukan Kusabunni, Tafkin Gawo, Alumdawa, Unguwar Mailete da Malamawa a nan ma su ka kora ƴan bindgan da ke wajen.

A jihar Katsina kuwa an samu nasarar kai hari garin Kore da ke ƙaramar hukumar Ɓatagarawa a nan ma su ka kuɓutar da wasu da aka yi garkuwa da su.

Mutane huɗu jami’an su ka yi nasarar kuɓutarwa waɗanda aka yi garkuywa da su a Unguwan Magudu da ke ƙaramar hukumar Ɗandume a jihar Katsina.

Jami’an sun samu nasarar ƙato makamai daga wajen ƴan bindigan tare da hallaka wasu yayin da aka kuɓutar da dabbobi da ake zargi masu garkwuan sun sace.

Continue Reading

Labaran jiha

Yara 10 Sun Rasa Rayukan Su Sakamakon Cutar Da Ta Bulla A Kaduna

Published

on

Kimanin yara 10 ne ‘yan tsakanin shekaru 3 zuwa 13 aka rahoto sun rasa rayukansu sakamakon bullar wata cuta mai shake numfashi a garin Kafanchan da ke karamar hukumar Jema’a ta jihar Kaduna.

 

Babban Daraktan lafiya (CMD) na asibitin ‘Sir Patrick Ibrahim Yakowa’, Dakta Isaac Nathaniel ne ya tabbatar da bullar cutar a Kafanchan inda ya ce har yanzun ba a gano musabbabin cutar ba.

 

Shugaban Karamar Hukumar Jema’a ta Jihar Kaduna, Honarabul Yunana Markus Barde, ya yi kira ga mazauna garin da su tashi tsaye sukai rahoton duk wani yaro mai shekaru kasa da 13 da ke fama da matsalar shakewar numfashi, ciwon makogwaro ko kuma yoyon majina a hanci ga hukumomin kiwon lafiya mafi kusa.

 

Shugaban ya bukaci mazauna garin da su lura da irin wadannan alamomin domin dakile yaduwar cutar da wuri kafin ta yi kamari.

 

Haka kuma an shawarci ma’aikatan kiwon lafiya a matakin farko a fadin kananan hukumomi, cibiyoyin maganin gargajiya, malaman addini, da iyaye da su dauki matakin da ya dace, ganin cewa, wasu iyaye da ‘yan uwa suna boye wasu daga cikin masu fama da cutar.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: