Shugaban ƙungiyar kafafen yaɗa labarai a jihar kano kuma shugaban gidajen rediyon Cool, Wazobia, Arewa Prince Aboki ne ya bayyana hakan yayin wani taro da aka yi a Africa House.

Ya ce ya zama wajibi a jinjinawa gwamnan ganin yadda yake bawa ƴan jarida haƙƙinsu ta hanyar basu damar gudanar da aiki yadda ya dace.

Ya ƙara da cewa saɓanin wasu jihohi da za a iske ana cin zarafin ƴan jarida tare da hanasu gudanar da aikinsu.

Prince Aboki ya tabbatar da cewar a shekaru biyar na gwamnatin Ganduje, babu wani ɗan jarida da aka ci zarafinsa ko hanashi gudanar da aikinsa.

Leave a Reply

%d bloggers like this: