Connect with us

Labarai

An cafke Maza 5 kan Zargin yiwa Yar shekara 10 fyade

Published

on

Daga Jamil Lawan Yakasai

Rundunar yan sandan Jahar Kaduna sun cafke maza biyar bisa zargin su da yin lalata da yarinya mekimanin shekaru 10

Matasan da sukafito daga karamar hukumar Igabi, jihar Kaduna sun ceci yarinya mai shekara 10 da haihuwa da wasu maza biyar su ke kwanciya da ita.

Rahotanni sun bayyana cewa daga cikin wadanda su ke lalata da karamar yarinyar har da mijin goggonta.
Mahaifin yarinyar nakasasshe ne wanda ba ya iya motsi.

Yanzu haka yarinyar da aka nemi 6ata mata rayuwa ta na karkashin kulawar Hajiya Rabi Salisu ta kungiyar Arida Foundation of Nigeria (AFN).

Haj Rabi Salisu wanda ta fito a wani fefen bidiyo da yanzu haka ke zagaye Duniya wanda yarinyar ta bayyana cewa mahaifiyar yarinyar sun rabu da mahaifinta.

Rabi Salisu takara da cewar yarinyar ta samu kanta a cikin wannan hali ne bayan mahaifiyarta ta kai ta kara wajen mijin ‘yar uwarta saboda ba ta zuwa talla idan aka tura ta.

Shi dai Bawan Allah ya yi amfani da damar da ya samu na kwabar yarinyar, ya kare da kawo wasu ‘yan uwansa har maza biyu wanda su ka rika lalata da yarinyar.

Daga baya wannan Baiwar Allah ta kai kuka wajen mahaifiyarta cewa ta na ganin jini idan ta yi bawali. Daga nan ne tsohuwarta ta ja-kunnen mijin yayartan da ya yi nesa da diyarta.

“Bayan ta koma ta cigaba da talla, sai kuma ta hadu da wani mutumi mai saida gwanjo, wanda ya saya mata takalmin zuwa makaranta, ya rika yin lalata da ita.”

“ Daga nan ne kuma sai wani mutumi mai gidan burodi ya shiga sahu, bayan ya saye shinkafar da ta ke sayarwa.”

An samu maza kusan biyar su na biyan bukatarsu da wannan yarinya.

Da manema labarai su ka tuntubi Rabi Salisu, ta ce yanzu ana kula da yarinyar sakamakon cututtukan da ta kamu da su, da kuma wasu rauni a bangaren al’aurarta.

Zuwa yanzu shugabar kungiyar ta AFN ta bayyana cewa an kama mutum hudu daga cikin wanda ake zargi, ana cigaba da bincike domin a gurfanar da su.

Jami’in hulda da Jama’a na rundunar ‘Yan sanda na Jihar Kaduna ASP Mohammed Jalige, ya ce mutane biyu daga ciki sun amsa laifinsu, sauran biyun ba su kai ga amsa laifin na su ba, sannan ana neman daya daga ciki Wanda ya tsere.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Zagon Kasan Da Kwankwaso Ya Yi Wa Jam’iyyar NNPP Ya Sa Ba Muyi Nasara A Kotuba- Alhaji Abbas

Published

on

Babban jigo a jam’iyyar NNPP, Alhaji Abbas Onilewura ya zargi dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso kan rasa nasarar jam’iyyar a jihar Kano.

 

A jiya Laraba 20 ga watan Satumba kotun ta yanke hukunci inda ta tsige Gwamna Abba Kabir na jam’iyyar a matsayin gwamna.

 

Kotun kuma ta tabbatar da Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

 

Yayin da ya ke martani kan hukuncin, Abbas ya ce Kwankwaso ya siyar da jam’iyyar lokacin da ya ke tattaunawa da APC kan mukamin minista a Abuja.

 

Onilewura ya bayyana haka ne a yau Alhamis 21 ga watan Satumba a cikin wata sanarwa da ya fitar.

 

Ya ce zagon kasa da Kwankwaso ya yi wa jam’iyyar ce ya jawo rashin nasararta a hukuncin kotun da aka yanke a jiya.

 

Ya kara da cewa Wannan rashin nasara babbar asara ce a jam’iyyar mu kuma hakan ya faru ne saboda son rai na Kwankwaso wanda ya siyar da jam’iyyar.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Delta Ta Amince Da Rage Kaso 25 Na Kudin Jami’a A Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Delta ta amince da rage kashi 25 na kudin makarantar daliban jami’a a jihar.

Wannan dai wani bangare ne na tallafin da gwamnatin za ta bai wa daliban kuma ya shafi jami’a hudu mallakin jihar.

Hakan na kunshe a wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan Festus Ahon ya sanyawa hannu ranar Laraba.

Sanarwar ta ce gwamnan ya bayar da umarnin bai wa ma’aikatan jihar tallafin naira dubu goma kowanne tsawon watanni uku.

Sannan an amince da kashe naira biliyan 5.522 ga ma’aikata 50,196 a matsayinalawus da aka yi musu karin matsayi.

Sannan gwamnatin za ta kashe naira biliyan goma wajen raba buhun shinkafa 17,000 da sama da buhu masara 60,000 ga marasa karfi.

Continue Reading

Labarai

Cibiyar Kare Hakkin Yan Jaridu Ta Yi Allah-Wadai Da Cin Zarafin Yan Jarida A Kano

Published

on

Cibiyar kare hakkin yan jarida ta duniya ta yi Alla wadai da cin zarafin yan jarida da wasu yan sanda su ka yi a Kano yau Laraba.

Salim Umar na jaridar Daily Trust da Zahradden Lawal na jaridar BBC an ci zarafinsu tare da lalata layan aikinsu yayin da us ke bakin aiki.

Babban jami’in kare hakkin yan jarida na duniya Melody Akunjiyan ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya aikewa manema labarai a yau.

Cibiyar ta ce abin takaici ne ganin yadda yan sandan su ka nuna rashin kwarewa ta hanyar cin zarafin yan jaridan yayin da su ke bakin aiki.

Cibiyar ta bukaci hukumar yan sanda ta kasa da su kula tare da kiyayewa a gaba wajen cin zarafin yan jarida musamman idan aiki ya hadasu da jami’an yan sanda.

Haka kuma cibiyar ta bukaci da aka ci gaba da bai wa yan sanda horo yadda za su dinga mu’amala da yan jarida tare da mutunta darajar dan adam.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: