Labaran ƙetare
Donald Trump– Democrat ta shirya Magudin zabe A Amurka


Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi zargin ‘yan Jam’iyyar Democrat na shirin tafka magudi a zaben shugaban kasar da zai gudana cikin watan Nuwamba mai zuwa.

Donald Trump wanda ke wannan zargi jim kadan bayan Jam’iyyarsa ta Republican ta kammala amincewa da takararsa karo na biyu a zaben shugaban kasar na watan Nuwamba, Wanda zasu kara da Dan takarar Democrat Joe Biden.
Donald Trump ya bayyana zargin ne a wurin taron da ya gudana a Jihar North Carolina inda ya ce yana da shakku kan zaben mai zuwa.

Trump ya bukaci ‘ya’yan Jam’iyyar sa ta Republican su bude idanun su saboda abinda ya kira yunkurin ‘yan Jam’iyyar Democrat na sace zaben wajen kara yawan masu kada kuri’u ta gidan waya.

Kuri’un jin ra’ayin jama’a na nuna cewa Joe Biden ke sahun gaba wajen shirin lashe zaben, yayin da Amurkawa ke cigaba da bayyana rashin amincewarsu da rawar da Trump ke takawa musamman wajen yaki da annobar COVID-19 da kuma matsalar tattalin arziki.

Labaran ƙetare
Wakilan Ƙasashen Duniya A Fannin Tsaron Sun Kammala Taron Don Shawo Kan Rikicin Ukraine


Wakilan kasashen duniya sun yi wani taro na duba hanyoyin kawo karshen rikicin da ke faruwa a Kasar Ukraine.

Masu bayar da shawara kan harkokin tsaro na ƙasashen da kungiyoyin duniya sun kammala taron tattaunawa a Jeddah dangane da abubuwan da ke faruwa a kasar Ukraine.
A ranar Asabar 5th ga watan Agusta wanda aka yi na kasashen duniya 40 da kuma wasu kungiyoyin duniya ne su ka halarta.


Wakilai a zauren Majalisar Dinkin Duniya sunhalarci taron.

Zaman ya gudana ne karkashin jagorancin karamin minista sannan mai bayar da shawara kan harkokin tsaro Dakta Mosaad Bin Mohammad Al-Aiban.
ki
Wadanda su ka halarci taron sun yabawa kasar Saudiyya bisa gayyato mutane sannan ta shirya tare da tsara taron a cikin kasar.
Taron na zuwa ne a wani bangare na sake daura damara tare da cigaba da kuma ƙara kaimi wanda yarima Mohammad Bin Salman Bin Abdulaziz ya aiwatar, kuma masarautar saudiyya ta shiga tsakani tun a watan Maris na shekarar 2022.
Kasashe da kungiyoyin da su ka aike da wakilcin sun hada da, Argentine Australia, Bahrain, Brazil, Bulgaria, Canada Chile, da kuma ƙasar China.
Sauran su ne hadaddiyar daular Comoros, Czech, Denmark, Egypt, Estonia, European Commission, European Council, Finland, Germany, French Republic, India, Indonesia, Japan, Hashemite, Jordan Latvia da kuma Qatar, Korea, South Africa, Lithuania.
Haka kuma akwai Italian, Kuwait, Netherlands, Norway, Poland, Korea, Romania, Turkey, Hadaddiyar daular larabawa, Amuruka, majalisar dinkin duniya da kuma kasar Ukraine.
Mahalarta taron sun gamsu da cigaba da tattaunawa tare da bayyana ra’ayi, domin samar da hanyoyin na dorewar zaman lafiya.
Sannan sun gamsu da yadda aka samar da cigaba a zaman da ya gabata.
Labaran ƙetare
Alhazan Najeriya 13 Sun Rasa Rayukan Su A Kasar Saudiyya


Akalla Alhazan Najeriya 13 ne suka rasa rayukansu a hajjin bana, yayin da mutane 41,632 suka kamu da rashin lafiya a Kasar Saudiyya.

Shugaban likitocin Najeriya mai kula da alhazai Dakta Usman Galadima ne ya bayyana haka a ranar Lahadi a garin Makka.
Usman ya ce sun kula da marasa lafiya 25,772 a filin Arfa yayin da suka kula da mutane 15,680 a Makkah da Madinah kafin ranar Arfa.

Usman ya kara da cewa mutane bakwai da suka fito daga jahohi daban-daban ne suka rasa rayukansu kafin Arfa .

Galadima ya ƙara da cewa mutanen da su ka rasa rayukansu sun fito ne daga Jihohi kamar haka Jihar Kaduna 2 Osun 2 Filato 1 Borno 1 Lagos 1 Yobe 1 Benue 1 sai kuma birnin Tarayya Abuja 1.

Kazalika Dr Usman ya ce suma jiragen yawo sun samu mutane uku da suka rasa rayukansu.
Sannan ya yi kira da a dakatar da hana tsoffi da kuma marasa lafiya zuwa gurin jifan shaidan sakamakon cinkoson da ake fuskanta.
A yayin jawabinsa Kwamishinan Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON Goni Sanda ya ce za su fara jigilar maniyyata zuwa gida Najeriya a ranar 4 ga watan Yulin da muke ciki zuwa ranar 3 ga watan Agusta.
Labaran ƙetare
Amurka Da Saudiyya Sun Zargi Bangarorin Da Ke Rikici A Sudan Da Watsi Da Sulhu A Tsakaninsu


Bayan sake sanya hannu kan yarjejeniyar dakatar da kai wa juna hare-hare a Sudan, an zargi bangarorin da ke rikici a kasar da sake yin watsi da batun sasanci a tsakaninsu.

Kasashen Amurka da Saudiyya, sun ce suna bincike kan bayanan da ke nuna cewa bangarorin kasar Sudan da ke yaki da juna, sun saba yarjejeniyar nan ta tsagaita wuta da suka cimma a baya-bayan nan.
Wannan na zuwa ne yayin da ake kokarin fara aikin samar da agajin jinkai gadan-gadan a Sudan.

Cikin wata sanarwa ta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu da ke kai komon ganin an sasanta rikicin na Sudan, sun ce bangarorin ba su mutunta abin da aka amince da shi na cewa babu batun afka wa juna tun kafin yarjejeniyar ta fara aiki a ranar Litinin.

Kwamitin da ke sa ido kan tsagaita wutar dai, ya fada a jiya Talata cewa a binciken da ya gudanar ya gano yadda aka yi fatali da abun da aka tsaya a kai game da dakatar da kai wa juna hare-haren.

Ƙasar Sudan na fama da rikici tun bayan da aka smau sabani a tsakanin manyan sojojin ƙasar biyu.
-
Mu shaƙata8 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada4 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare4 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai4 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Labarai6 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?
-
Girke girke5 years ago
YADDA AKE LEMON SHINKAFA