Corona VirusCorona Virus

A yayin da kasashen Turai ke cigaba da yin gwaje-gwaje ingancin maganin Korona da suka hada, Najeriya ma ba a barta a baya ba wajen hadawa da yin nata gwajin magungunan.

Sai dai Hukumar kula da Ingancin Abinci Da Magunguna ta Kasa (NAFDAC) ta bayyana cewa tana yin gwajin magungunan warkar da Korona har guda 40 da masu hada magungunan gargajiya suka mika wa hukumar.

Shugabar hukumar Mojisola Adeyeye ta sanar da haka tana mai cewa ana yin gwajin ingancin magungunan ne saboda tabbatar da ingancin maganin da Alumna zasu yi amfani dashi.

” Haka kuma NAFDAC ta gindaya musu wasu sharudda da dokoki da za su bi wajen hada maganin.

Za dai a fara a yin gwajin ingancin magungunan akan dabbobi a karon farko tukunna.

Mojisola ta gargadi masu maganin kada su kuskura su jaraba wani magani ba tare da hukumar ta bada daman haka ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: