Connect with us

Labarai

Najeriya ta ja Kunnen Mahukuntan Ghana Kan Muzgunawa yan Najeriya

Published

on

Najeriya ta aika wa gwamnati da mahukuntan kasar Ghana da sakon jan kunne sakamakon muzgunawa dan Najeriya da ƙasar ke yi.

Ministan yada Labarai, Lai Mohammed yayi wannan gargadi ta cikin wani sako da ya fitar.

sanarwar da Lai Mohammed ya fitar ya ce yanzu haka sakon ya isa ga gwamnatin Ghana har kwace ofishin jakadancin Najeriya tayi dake titin Barnes dake babban birnin kasar, Accra.

sannan kuma ta sake zuwa ta rusa wani gini mallakin gwamnatin Najeriya dake titin Julius Nyerere a kasar.
” Bayan haka, shekaru uku kenan duk shekara sai kasar ta dawo da daruruwan dan Najeriya gida wai basu da takardun zama a kasar ko kuma basu shiga ƙasar bisa ka’ida ba.

” Sannan kuma mahukunta a kasar na bi suna garkame shagunan dan Najeriya babu gaira babu dalili, bayan ta zabga musu kuɗin haraji.

Kazalika gwamnatin ta yi wa dokokin zaman kasar garambawul da yanzu ta tsawwala kudin sabunta lasisin zama a Ƙasar duk shekara wanda a Najeriya dan ƙasar Ghana naira 7000 kacal yake biya kuɗin zaman kasar.

Haka kuma da gangan mahukuntar kasar suke tsananta shari’a akan Dan Najeriyan da ya fada hannun su.

Zuwa yanzu akalla mutum 200 dan Najeriya na kulle a gidan Kaso na Kasar.
A daga karshe Lai Mohammed yace gwamnati bazata lamunci irin cin zarafin da ake wa alummarta ba.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

‘Yan Takarar Gwamnoni A Jam’iyyar PRP Sun Koma SDP

Published

on

‘Yan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar PRP a zaben 2023 na sun sauya sheka zuwa jam’iyyar SDP.

Shugaban kungiyar ‘yan takarar gwamnan a PRP Malam Hayatuddeen Lawai Makarfi ya tabbatar da ficewarsu daga PRP zuwa SDP.

Shugaban kungiyar ya bayyana cewa sun dauki matakin koma SDP ne domin tsamo kasar nan daga halin da take ciki.

Lawai Makarfi wanda ya yi takarar gwamna a jam’iyyar ta PRP a Jihar Kaduna, ya bayyana cewa mutane na sauya sheka zuwa SDP ne bisa yadda da shugabancinta.

Makarfi ya ce sauya shekar su wani shiri ne na hadin domin kubtar da Najeriya daga shugabanci mara kyau, inda kuma ya nuna damauwarsa bisa yadda ake ci gaba da samun zubar jini, karuwar takauci, ya yin da hukumomin gwamnati ke durkushewa, inda kuma jam’iyyar APC da PDP suka mayar da mulkin kasar tamkar kasuwanci.

Kungiyar ‘yan takarar gwamnan ta kuma mika godiyarta ga PRP bisa damar da ta ba su a siyasa, inda suka ce a halin yanzu sun koma kan hanyar gaskiya.

Shugaban jam’iyyar SDP Malam Shehu Musa Gabam ya shaida musu cewa jam’iyyar za ta bai’wa masu sauya shekar dukkan wata dama da ta kamata.

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kaduna Za Ta Dauki Ma’aikatan Lafiya Sama 1,000

Published

on

Gwamnatin Kaduna Jihar ta amince da daukar ma’aikatan lafiya 1,800 a fadin Jihar.

Kwamishiniyar lafiya ta Jihar Hajiya Umma Ahmad ce ta tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Alhamis.

Sanarwar ta ce gwamnatin Jihar karkashin jagorancin gwamna Malam Uba Sani za a dauki Ma’aikatan ne domin cike gurbin Ma’aikatan a dukkan cibiyoyi kiwon lafiya matakin farko na Jihar.

Sanarwar ta kara da cewa daukar Ma’aiktan hakan zai kara tabbatar da ci gaban Jihar akan matsayin da ta ke dashi a fannin kiwon lafiya matakin farko a Najeriya.

Kwamishinyar ta kuma ce daukar ma’aikatar zai kawo karshen karancin ma’aikata da ake samu a cibiyoyin kiwon lafiyar, tare da raguwar yawaitar mace-macen mata masu juna biyu da kananan yara, da kuma kara inganta lafiyar mutanen Jihar.

Acewarta a halin yanzu ana ci gaba da gyaran cibiyoyi 255 na kiwo lafiya matakin farko, yayin da za a daga martabarsu zuwa mataki na biyu, da samar da kayan aiki na zamani, tare da bayar da muhimman magunguna duk a kokarin da gwamnatin Jihar ke yi na inganta bangaren kiwon lafiya.

Kwamishinar ta kuma ce cibiyoyin za su dunga aikin duba masu cutuka daban-daban da suka hada da ciwon suga da bai yi karfi ba, hawan jini shima da bai yi karfi ba, da bayar da tallafin wajen haihuwa da dai sauransu.

Continue Reading

Labarai

Majalisar Wakilan Za Ta Haramtawa Masu Shekaru Sama Da 60 Tsayawa Takara

Published

on

Majalisar wakilan Najeriya ta tsallake karatu na biyu kan kudurin da zai haramtawa ‘yan takarar shugaban Kasa, da na gwamnan masu shekaru sama da 60 tsayawa takara.

A zaman Majalisar na yau Alhamis, da kudurin ya tsallake karatu na biyu, bayan da dan Majalisar Hon Ikeagwuonu Ugochinyere ya dauki nauyin kudurin da ke bukatar canza wasu bangarori na kudin tsarin mulkin Kasa na shekarar 1999.

Rahotanni sun bayyana cewa da zarar kudurin ya tsalle karatu na uku, kuma shugaban Kasa ya sanya hannu akansa, hakan zai sauya fasalin tsayawa takara a Kasar.

Daga cikin abubuwan da kudurin ya kunsa sun hada da, dukkan wanda ya haura shekaru 60 da haihuwa b azai tsaya takarar shugaban Kasa ba, ko gwamna a Kasar.

Sannan kuma wajibi dukkan dan takara ya kasance ya mallaki shedar digirinsa na farko a bangaren da ya fi kwarewa akai, a matsayin mafi karancin takardar karatu.

Ya yin da kuma kudin ya bukaci yin gyara a sashe na 131 na kudin tsarin mukin Kasa, na bukatar iyaknce shekaru ga kowanne dan takarar shugaban Kasa, tare da sashi na 177 ga gwamomin Jihohi.

Baya ga wannan kuduri majalisar ta kuma amince da wasu kudurori daban-daban da suka shafi ci gaban Najeriya.

 

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: