Connect with us

Labarai

SERAP ta Maka Buhari a Kotu kan Biliyan 800

Published

on

Kungiyar Kwato Hakki da Sa-ido Kan Hana Rashawa da kididdiga(SERAP), ta maka Shugaba Muhammadu Buhari a Babbar Kotun Tarayya, Abuja, inda ta nemi ta tilasta wa Shugaba Muhammadu Buhari bayyana sunayen wadanda gwamnatin sa ta kwato zunzurutun naira bilyan 800 daga hannun su.

A cewar kungiyar Buhari da bakin sa ya bayyana cewa gwamnatin sa ta “kwato naira bilyan 800 daga hannun barayin gwamnati.

Buhari ya yi wannan jawabi a cikin takardar da ya karanta, a ranar 12 Ga Yuni, ranar Dimokradiyya, inda ya kara da cewa, “Ana ci gaba da zuba kudaden cikin ayyukan raya kasa da gwamnati ke aikatawa.”

Cikin karar da SERAP ta shigar, ta nemi kotu ta tilasta Buhari ya bayyana sunayen barayin gwamnati da aka kwato naira bilyan 800 a hannun su.

Kazalika Shugaba Buhari ya bayyana naira nawa aka kwato ga kowane mutum daya.
Haka kuma kotun ta tilasta Shugaba Buhari ya bayyana ranakun da aka karbo ko nawa ne daga hannun kowane barawon gwamnati.

Serap ta bukaci kotu ta sanya Buhari ya fito ya bayyana dukkan ayyukan da ya ce an yi da kudaden da kuma inda aka yi ayyukan.
Sannan ya bayyana farashin da aka bayar da kowace kwangilar da aka biya a cikin kudaden.

SERAP ta ce ‘yan Najeriya na da hakkin sanin yadda aka yi da kudaden da kuma sanin barayin kasarnan , tare da sanin adadin naira nawa kowanen su ya sata.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

An Kone Ofishin Yan Sanda A Anambra

Published

on

Wasu ƴan daga sun kai hari tare da ƙone ofishin ƴan sanda a jihar Anambra.

 

An kai harin ne ofishin ƴan sanda na Neni da ke ƙaramar hukumar Anaocha a jihar da misalin ƙarfe 02:00am na dare wayewar yau Alhamis.

 

Mai magana da yawun ƴan sanda a jihar Tochukwu Ikenga ya ce mutanen sun kai harin ne da abin fashewa da ake zargi bam ne.

 

Sannan ya ce maharan ba su ɗauki makaman jami’an ko yin garkuwa da jami’an su ba.

 

Ya ƙara da cewa, maharan sun gudu bayan da ƴan sanda su ka ci ƙarfinsu.

 

Zuwa yanzu ana ci gaba da hibiya don gano su waye su ka kai harin tare da kamasu.

 

Sai dai bai bayyana asarar da aka yi ba a sakamakon harin da aka kai.

 

 

Continue Reading

Labarai

An Kama Ƴan Fashin Da Su Ka Yi Wa Matar Aure Fyaɗe A Jigawa

Published

on

Rundunar ƴan sanda a jihar Jigawa sun kama wasu mutane uku da ake zargi da aikata fashi da makami haɗi da fyaɗe ga matar aure a jihar.

 

Kwamishinan ƴan sandan jihar AT Abdullahi ne ya bayyana haka yau Alhamis.

 

Ya ce an kama mutane uku bayan da su ka shiga gidan wani Mudan Ibrahim mazaunin ƙauyen Chori a ƙaramar hukumar Ringim tare da yi masa fashi daga bisani su ka yi wa matarsa fyaɗe.

 

Ƴan sandan sun samu labarin ne a ranar 17/03/2024.

 

Bayan zurfafa bincike, jami’an sun kama wani Umar Ibrahim, Umar Nasara, da wani Abubakar Isah dukkaninsu mazauna ƙauyen Chori a jihar.

 

Tuni aka ci gaba da zurfafa bincike a kai, kuma da zarar an kammala za su gurfanar da su a gaban kotu kamar yadda kwamishinan ya shaida.

 

A wani labarin kuma kwamishinan ya bayyana nasarar kama wasu ƴan fashi da makami, da kuma wasu da ake zargi da aikata sata a jihar.

 

 

Continue Reading

Labarai

Malamin Makaramtar Firamare Na Kuriga Ya Mutu A Hannun Ƴan Bindiga Kafin Kuɓutar Da Dalibai

Published

on

Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya sha alwashin ɗaukar nauyin karatun ɗalibai 137 da aka kuɓutar daga hannun ƴan bindiga.

 

Ɗaliban su ne waɗanda aka yi garkuwa da ssu daga makarantar firamare ta Kuriga a jihar.

 

Gwamnan ya ce zai ɗauki nauyin karatun nasu ne daga matakin Firamare zuwa sakandire ƙarƙashin cibiyar Uba Sani Foundation.

 

Gwamnan ya bayyana haka yau Alhamis kafin mayar da ɗaliban zuwa Kuriga.

 

Ya ce bayan kuɓutar da su, an ɗauki lokaci domin duba lafiyarsu kafin miƙasu ga iyayensu.

 

Ya ce guda cikin malaman da aka yi garkuwa da su mai suna Malam Abubakar, ya rasa ransa a hannun ƴan bindigan.

 

A sakamakin haka, gwamnan ya ce zai ɗauki nauyin karatun ƴaƴan malamin, tare da bai wa iyalansa naira miliyan goma.

 

Akwai waɗanda su ka samu larurar kwakwalwa daga cikin ɗaliban da aka kuɓutar, a don haka su ka miƙasu ga kwararrun likitoci domin duba lafiyarsu.

 

Sannan gwamnatin ta bayar da umarnin yin wasu ayyuka a Kuriga, wamda gwamnan ya ce garin na daga cikin garuruwan da su ka fi zaman lafiya a jihar.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: