Connect with us

Labarai

An jinjinawa Ganduje wajen kare martabar Annabi S.A.W da addinin Allah

Published

on

Sarkin Sharifan Kano Ya Yabawa Gwamna Ganduje Wajen Kare Martabar Annabi Muhammad (SAW) Da Addinin Allah

Kwanan baya ne Sarkin Sharifan Kano Sidi Fari ya yabawa hobbasar da Gwamnan jihar ta Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ke yi wajen kare martabar Annabin Tsira Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam da kuma kokarin da ya ke wajen ganin Addinin Musulunci ya kara habaka.

A yayin da Gwamnan yake karbar tawagar Sharifan daga Zawiyyoyi da majalisun Sharifan daga fadin jihar ta Kano a babban dakin taro na Africa House, da ke Gidan Gwamnatin Kano, ya kara tabbatar musu da cewa ire-iren addu’o’in da su ke yi ne tare da malamai da ke jihar da daukacin al’umma, shine jihar ta ke cikin zaman lafiya.

Gwamnan ya yi dan tsokaci kadan wajen irin gudummmawar da Sharif Sheikh Abdulkareem Al-Maghili ya bayar wajen tabbatuwar adalci a mulkin jama’a da kuma bayar da tsari na musamman wajen yadda sha’anin mulki ya kamata ya zamo, tun daga lokacin da ya shigo wannan jiha ta Kano.

Ya ce “Wannan dalilin ne ya sa mu ka sa wa Hukumar Shari’ah ta jiha da sunan Sheikh Al-Maghili. Domin tunawa da irin gudummawar da ya bayar a wannan jiha ta mu ta Kano. Sannan wani abin alfahari kuma shine, kasancewarsa shi ma Sharifi jinin Ma’aikin Allah Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam.”

Ya kuma tabbatarwa da Sarkin Sharifan cewa gwamnatin Kano za ta karasa ginin Zawiyyar Fadhima dake Kantudu a unguwar Sharifai. Baya ga kira da Sarkin Sharifan ya yi fa gwamnati da ta shigo wajen ganin kammaluwar ginin.

“Mu na kuma kara godiya wajen yi mana addu’o’i na musamman da a ka yi lokacin da mu ke tsananin fuskantar annobar COVID-19. Alhamdulillah mu na da labarin irin addu’o’i da a ka dukufa a ka yi mana gaba daya. Wannan ya kara nuna yadda ku ke da kishin wannan jiha ta mu da ma kasa baki daya,” in ji Gwamnan.

Da ya yi magana a madadin Sarkin Sharifan, Shugaban Majalisar Dattawa ta Shurafa’u a Kano, Sharu Tijjani Ibrahim, ya tabbatarwa Gwamnan na Kano, jin dadin da Sharifan Kano suke ji saboda kulawa ta musamman da gwamnatin Ganduje ke ba su. “Tare da share mana kukanmu duk lokacin da mu ka kawo kukanmu ga Maigirma Gwamnan Jihar Kano,” ya ce.

“Maigirma Gwamna mu na kara nuna maka goyon bayanmu wajen kokarin da kake don ci gaban wannan babbar jiha ta mu ta Kano. Kullum ba ma gajiyawa wajen yi maka addu’o’I saboda neman tallafi daga Allah, Ya sa ka gama lafiya,” in ji shi.

Daga karshe Sarkin Sharifan ya yi wata addu’a ta musamman ga Gwamna Ganduje. Shi kuma Gwamnan ya kara yabawa da Sharifan saboda wannan babbar ziyara da su ka kawo masa har fadar gwamnati.

Abba Anwar
Babban Sakataren Yada Labarai
Na Gwamnan Jihar Kano
Laraba, 2 ga Watan Satumba, 2020
cps@kanostate.gov.ng
fatimanbaba1@gmail.com

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Tsadar Karatu Na Iya Sa Rabin Ɗaliban Jami’a Su Gudu – ASUU

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ta ce kashi 50% na ɗaliban da ke karatu na iya ajiyewa saboda tsadar karatu da ake ciki a ƙasar.

Shugaban ƙungiyar Frafesa Emmanuel Osodoke ne ya bayyana haka ya ce nan da shekaru biyu zuwa uku masu zuwa ɗaliban da ke karatu a jami’o’in ƙasar kashi 50% daga ciki na iya ajiye karatun nasu.

A wata hira da aka yi da shugaban a gidan talabiji na Channels ranar Lahadi da daddare, ya gargaɗi ɓangaren ilimi na ƙasar da su farga a kan abinda ka iya faruwa.

Sai dai ya alaƙanta ƙara kuɗin da jami’o’i su ka yi da mafi ƙarancin albashin da ake biya na naira 30,000 a ƙasar.

Sannan ya ce akwai hatsari mai yawan gaske idan aka samu ƙarin matasa masu yawa da su ka bar makaranta.

Idan ba a manta ba, a makon da ya gabata gwamnatin Najeriya ta ce ta ƙarawa malaman jami’a albashi da kashi 30 ga masu matsayin farfesa.

Continue Reading

Labarai

Gobara Ta Kama A Kotun Ƙoli Ta Najeriya A Abuja

Published

on

Rahotanni daga baban birnin tarayyar Najeriya Abuja na tabbatar da cewar kotun ƙoli ta kama da wuta.

Ofishin alƙalai uku aka ruwaito sun ƙone bayan tashin gobarar.

Godan jaridar Arise ya ruwaito cewar, wutar ta kama wai ɓangare na cikin kotun.

Sai dai ba a san sanadin tashin gobarar ba.

Wannan dai itace gobara da aka yi a kusa-kusa wadda ta shafi ofishin gwamnati.

Ko a watan Mayun shekarar da mu ke ciki, gobara ta kama a rundunar sojin samar Najeriya.

Yayin da a shekarar da ta gabata ta 2023 ma’aikatar kuɗi ta tarayya wani ɓangare ya kama da wuta.

Continue Reading

Labarai

Amuruka Ta Gargaɗi Ƴan Ƙasar Mazauna Najeriya Kan Ziyartar Wasu Jihohi Har Da Kano

Published

on

Ƙasar Amurka ta gargaɗi ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su kiyaye wajen ziyartar wasu jihohi da ka iya faɗawa cikin hatsari.

Sanarwar na zuwa ne bayan gudanar da wani bincike da su ka gano an samu ƙaruwar aikata manyan laifuka a jihohin.

Jihohin sun haɗa da Borno, Adamawa, Yobe, Kogi, Bauchi, Kaduna, Kano, Gombe, Bayelsa, Rivers, Enugu da jihar Bayelsa.

Sauran jihohin su ne Imo, SokOto, Zamfara, Katsina, da jihar Abia.

Ƙasar ta gargaɗi mutanenta da su kiyaye wajen ziyartar waɗannan jihohi domin su na iya faɗawa cikin tarkon masu garkuwa da mutane ko wasu miyagun laifuka.

Binciken da su ka yi sun gano cewar masu satar mutane domin neman kuɗin fansa na amfani da ƙarin mutane a wasu sassa domin cimma muradinsu.

Sannan gwamnatin Amurukan ta buƙaci ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su ƙara sanya idanu a kan dukkanin zirga-zirgarsu don gudun faɗawa hatsari.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: