Siyasa
Adam Zango zai yiwa Atiku waƙar kiranye idan kowa ya tura 500
Mawaƙin ya wallafa hakan ne a shafinsa na Instagram cewa yanaa so ya yi zazzafar waƙa don yowa Atiku kiranye.
Fitaccen mawaƙi kuma jarumi a masana antar fina finan Hausa Adam Zango ne ya bayyana hakan cikin wani faifan bidiyo da yayi.
Ya ce tunda aka yi zaɓe tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya tafi dubai, kuma yana son yin waƙar ne don yi masa kiranye.
Ya cigaba da cewa a wannan lokaci ba su samu abinda suke buƙata ba a dangane da zaɓen da aka yi a shekarar 2019, don haka ya nemi masoyan Atiku ƴan Najeriya da kowanne mutum guda ya tura naira 500 don yiwa Atiku waƙa.
Hakan na zuwa ne kwana ɗaya rak da tattaunawarmu da mawaƙi Dauda Kahutu wanda aka fi sani da Rarara da ya nemi masoya Buhari su tura naira 1000 kowanne don yiwa shugaban kasar waƙa tare da nuna ayyukan da ya yiwa kasa.
Leave a Reply
Siyasa
Jam’iyyar APC Ta Zargi Gwamnatin Kano Da Almundahanar Kuɗaɗe
Jam’iyyar APC da gwamnatin jihar Kano sun yi musayar yawu kan zargin wani shiri na karkatar da sama da Naira biliyan Takwas na kuɗin ƙananan hukumomin jihar.
Shugaban jam’iyyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas, a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Abuja, ya yi zargin cewa gwamnatin jihar na ƙoƙarin karkatar da naira biliyan 8,080,190,875.13.
A cewarsa rashin tabbas kan abin da zai kasance sakamakon hukuncin da kotun ƙoli ta yanke kan zaɓen gwamnan jihar ya sanya gwamnatin ɗaukar wannan matakin.
Shugaban jam’iyyar APC ya kuma gargadi ƙananan hukumomi da bankunan kasuwanci da su dakatar da shirin fitar da kuɗaɗen.
Jaridar Daily Trust ta ce da yake mayar da martani, kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Baba Halilu Dantiye, ya bayyana cewa.
Sannen abu ne cewa gwamnatin jihar Kano a ƙarƙashin ingantaccen shugabancin Injiniya Abba Kabir Yusuf, a cikin watanni bakwai da suka gabata ta yi suna wajen ganin an tabbatar da gaskiya da adalci da amfani da dukiyar al’umma yadda ya dace.
Ya kara da cewa gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ba za ta bari mutanen da ke jin zafi ba domin faɗuwa zaɓe kaɗai ba, amma saboda sun yi asarar hanyoyin satar dukiyar gwamnati su ɗauke mata hankali ba.
Siyasa
Allah Ya Zaɓa Wa Al’ummar Kano Mafi Alheri A Kotun Ƙoli – Sanata Shekarau
Tsohon gwamnan jihar Kano, Ibrahim Shekarau ya tofa albarkacin bakinsa game da shari’ar zaben da ake yi a kotun koli.
A wata zantawa da aka yi da shi, Sanata Ibrahim Shekarau ya ba gwamna Abba Kabir Yusuf da Nasiru Yusuf Gawuna shawara.
Babban ‘dan siyasar ya yi kira ga gwamna mai-ci da Nasiru Yusuf Gawuna da kotu ta ce shi ya lashe zabe da su koma Allah SWT.
Malam Shekarau ya bukaci ‘yan siyasar su roki zabin Ubangiji kuma su karbi duk kaddarar da ta auka masu bayan hukuncin kotu.
Rohoton na zuwa ne a daidai lokacin da ake jiran kotun koli ta yi hukunci karshe a shari’ar zaben gwamnan na jihar Kano.
Tsohon Ministan ilmin ya yi magana a Rumfar Afrika, ya ce abin da ya fi dacewa shi ne ayi addu’ar zabi mafi alheri ga mutanen Kano.
Shekarau wanda ya yi gwamna tsakanin shekarar 2003 da 2011 ya yi wannan addu’ar, sannan ya ce yana fatan APC da NNPP za su yi irin haka.
Siyasa
Muna Da Ƙwarin Guiwar Samun Nasara A Kotun Ƙoli – Abba Kabir Yusuf
Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya bayyana kwarin gwiwarsa a game da hukuncin Kotun Koli.
Abba Kabir ya bayyana haka ne a jiya Lahadi 24 ga watan Disamba a filin wasa na Sani Abacha yayin bikin horas da matasa 2,500 a jihar.
Gwamnan ya yabawa alkalan kan yadda suka dage don ganin sun yi adalci kan shari’ar da ke gabansu.
Ya kuma yi kira ga jama’ar jihar da su kwantar da hankalinsu da kuma kara musu karfin gwiwa kan alkalan kotun.
Abba Kabir ya tabbatar wa magoya bayansa cewa ya na da tabbacin samun nasara a shari’ar da za a yanke.
Wannan na zuwa ne bayan da kotunan baya su ka soke nasararsa.
Gwamnan ya sake daukaka kara zuwa Kotun Koli inda a ranar Alhamis 21 ga watan Disamba ta zauna domin sauraron korafin
-
Mu shaƙata1 year ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai1 month ago
Mafi Karancin Sadaki A Najeriya Ya Koma Dubu 99,241
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini4 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
yusifhassan18@gmail.com
September 12, 2020 at 11:30 am
where is the account number please