Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya ta janye ƙarin kuɗin wutar lantarki

Published

on

A sakamakon janye ƙarin farashin ƙungiyar kwadago ta janye yajin aikin da ta shirya tsunduma a yau.

Gwamnatin tarayya ta janye ƙarin kuɗin wutar lantarki a daidai lokacin da ƙungiyar kwadago ta shirya tsunduma yajin aiki.

Ƙaramin ministan kwadago a Najeriya Festus Keyamo ne ya sanar da hakan a shafinsa na tiwita.

Wannan ne dalilin da ya sa ƙungiyar kwadago a Najeriya NLC ta janye tsunduma yajin aikin da ta shiya shiga a yau Litinin.

Sai dai janyewar ƙarin farashin wutar iya na makonni biyu ne kacal, kafin gwamnatin ta yi duba a bisa matakin da za ta ɗauka na gaba.

Ƙungiyar kwadago ta shirya shiga yajin aikin ne sakamakon ƙarin farashin wutar lantarki da man fetur wanda ta yi makonni biyu da suka wuce.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Gwamnatin Osun Za Ta Rage Kashi 50 Na Kudin Shinkafa Ta Saidawa Yan Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Ogun za ta fara siyarwa da ƴan jihar shinkafa tare da yin rahin kashi hamsin na kuɗin da ake siyar da ita a kasuwa.

 

Gwamnan jihar Prince Dapo Abiodun ne ya samar da haka, ya ce gwamnatinsa za ta yi hakan ne domin rage raɗaɗin matsin tattalin arziƙi da akee fama a jihar.

 

Gwamnan ya ceza a fara siyarwa da ma’aikatan gwamnatin jihar shinkafar a farashi mai rahusa, domin sauƙaƙa musu kan halin da ake ciki.

 

Gwamnan wanda ya yi bayanin yayin buɗe bakin azumi ranar Talata, ya ce dukkanin ma’aikatan gwamnatin jihar za su samu shinkafar a wannan farashi.

 

Tuni aka kafa kwamitin da zai kula da harkokin siyar da shinkafar ga ma’aikatan.

 

Sannan an gwamnatin za ta fara da siyarwa da ma’aikata ne daga bisani a kai ga sauran mutanen ƴan asalin jihar.

 

Kuma an ɗauki matakin yin rangwamen ne domin ɗorewa da cigaba da siyarwa mutanen jihar a farashi.

 

A cewar gwamnan, idan aka ce za a raba abincin kyauta lamarin ba zai ɗore ba.

 

Sai dai gwamnan ya ce za a baiwa talakawa da tsofaffi da ba za su iya siya ba shinkafar kyau

 

 

Continue Reading

Labarai

Sojoji Sun Hallaka Ƴan Bindiga Da Boko Haram A Katsina Da Borno

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta samu nasarar hallaka ƴan bindoga da mayaƙan Boko Haram a jihohin Borno da Katsina.

 

An hallaka mutane uku da ake zargi na daga cikin ƙungiyoyin a jihohin biyu.

 

Sannan an samu nasarar kuɓutar da dabbobi masu yawa bayan da aka hallakasu.

 

A wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau Laraba, ta ce nasarar na zuwa ne bayan musayar wuta da maharan.

 

Sannan sun samu nasarar ne a jiya Talata wanda ta kai ga kwato bindigu biyu ƙirar AK47 da harsasai masu yawa.

 

A cikin jawabin sanarwar, rundunar ta ce sun kai harin ne a Garin Rinji da ke ƙaramar hukumar Batsari, da kuma yankin Gori a ƙaramar hukumar Gwoza ta jihar Borno.

 

Haka kuma akwai babur guda ɗaya da rundunar ta kwato.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Juma’a Da Litinin Matsayin Ranar Hutu Ga Ma’aikata

Published

on

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana ranakun Litinin da Juma’a a matsayin ranar hutu ga ma’aikata.

 

Za a yi hutun Esta a ranakun Juma’a 29 ga watan Maris da kuma Litinin 1 ga watan Afrilu mai kamawa.

 

Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo ne ya sanar da hutun yau a madadin gwamnatin tarayya.

 

A sanarwar mai ɗauke da sa hannun Dakta Aishetu Gogi-Ndayako sakatariyar din-din-din a hukumar, sanarwar ta hori yan ƙasar da su kasance masu yafiya, nuna soyayya a ranakun hutun.

 

Sannan aka bukaci mabiya addinin kisita da su yi amfani da lokutan wajen kawo cigaba mai ma’ana a Najeriya.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: